Wasu ’yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 a wani harin kwanton-ɓauna da suka yi wa ayarin motocin ɗaukar kaya a yammacin Jamhuriyar Nijar, kusa da iyakar ƙasar da Mali, kamar yadda mazauna yankin suka bayyana a ranar Lahadi.
Wasu majiyoyi a Nijar sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Lahadi cewa, maharan sun kashe mutanen ne a cikin wannan mako bayan sun tare ayarin motocin a gundumar Banibangou da ke yankin Tillabéri, yankin da yake fama da ’yanta’adda masu alaƙa da ƙungiyar Al-Qaeda.
“An tsayar da manyan motoci biyar masu ɗauke da fasinjoji da kaya a yammacin ranar Juma’a. Maharan sun kashe maza 16, amma suka ƙyale mata,” in ji wani mazaunin Banibangou yayin tattaunawa da AFP.
Mutumin ya ƙara da cewa motocin sun taso ne daga birnin Yamai a kan hanyarsu ta zuwa Tizigorou, kuma harin ya auku ne a wani yanki na “hamada” mara nisa daga garin.
Sace motoci
Wani mazaunin maƙociyar gundumar Tondikiwindi ya shaida wa AFP cewa mutanen na kan hanyarsu ta zuwa kasuwar mako-mako, kuma “mata ne kaɗai aka bari da rai.” Daga cikin mutane 16 da aka kashe, har da wasu “yan kasuwa na yankin.”
Maharan, waɗanda har yanzu ba a san ko su wane ne ba, sun yi awon-gaba da motoci uku maƙare da kaya, sannan suka ƙona mota ɗaya.
Wannan hari ya zo ne bayan an kwashe watanni ana samun kwanciyar hankali a yankin Banibangou, inda ’yanta’adda suka ƙaddamar da jerin munanan hare-hare kan fararen-hula tsakanin shekarar 2021 zuwa 2023—a ƙauyuka, gonaki, kan hanyoyi, har ma da cikin masallatai.
Tallafi daga fararen-hula
A ranar Jumma’a, gwamnatin Nijar ta sanar da cewa za ta amince da kafa dakarun sa-kai na fararen-hula domin taimaka wa rundunar sojin ƙasar wajen yaƙi da ƙungiyoyin ta’addanci.
“Mun yi nasarar samar da tsaro. Jaruman dakarunmu na tsaro da kariya suna da iko a ƙasa, duk da hare-haren da ƙasarmu ta fuskanta,” in ji Shugaba Abdourahamane Tiani a makon da ya gabata.
Baya ga wannan yanki na yamma, Jamhuriyar Nijar na fuskantar hare-hare daga ’yanta’addan Boko Haram a kudu maso gabashin ƙasar.
AFIRKA
2 minti karatu
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali
Wannan hari ya zo ne bayan an kwashe watanni ana samun kwanciyar hankali a yankin Banibangou, inda ’yanta’adda suka Ƙaddamar da jerin munanan hare-hare kan fararen-hula tsakanin shekarar 2021 zuwa 2023 a ƙauyuka, gonaki, hanyoyi, har da masallatai.
Rumbun Labarai














