Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Amurka na ɗaukan matakai cikin sauri wajen kawo ƙarshen yaki da Iran.
"Za mu kawo ƙarshen wannan yaƙi cikin gaggawa. Suna matukar son yin yarjejeniya, sun gaji da wannan yaƙi," kamar yadda Trump ya faɗa a Fadar White House.
"Ina tunanin za mu gama da wannan cikin gaggawa, kuma ba za su sami makamin nukiliya ba, kuma ina fatan za mu kammala shi cikin yanayi mai kyau," kamar yadda ya kara bayyanawa.
Shugaban ƙasa ya kuma jaddada ƙarfin soja na Amurka, yana mai danganta hakan da ayyukan kwanan nan da suka rage ƙarfin Iran.
“Sojojinnmu shi ne mafiya karfi a duniya… Mun kawar da sojojin ruwansu. Sojojinsu na ƙasa sun tafi. Makamansu na harbo jiragen sama sun tafi. Dukkan kayan yaƙin da suke amfani da su don yaƙi ba bu su... Ba na son na ce shugabanninsu sun tafi, saboda ba abu ne mai kyau ba, amma hakan gaskiya ne,” in ji shi.
Trump ya jaddada cewa ba za a bar Iran ta samar da makamin nukiliya a kowane yanayi ba.
"Ba za mu iya barin hakan ta faru ba, kuma ba za mu jure masa ba," in ji shi.
Wannan ci gaban ya zo ne a daidai lokacin da tashin hankali a yankin ya ƙaru tun bayan da Amurka da Isra'ila suka kai hare-hare kan Iran a watan Fabrairu.
Tehran ta mayar da martani da hare-hare kan Isra'ila da kuma ƙawayen Amurka a yanki Tekun Fasha, tare da rufe mashigar Hormuz.
An samu yarjejeniyar tsagaita wuta da ta fara aiki a ranar 8 ga Afrilu ta hanyar shiga tsakani da Pakistan ta yi, amma tattaunawa a Islamabad ba ta samar da yarjejeniya mai ɗorewa ba. Daga bisani Trump ya tsawaita yarjejeniya ba tare da iyaka ba.












