| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
4 minti karatu
Iraniyawa sun nuna juriya da ƙalubale irin na lokacin yaƙi a wani gagarumin gangami a Tehran
Titunan birnin Tehran sun cika maƙil da bukukuwa, inda aka jera ƙofofin balan-balan masu launuka da kayatarwa tsawon kilomitoci, tutocin Iran suna kadawa, da kuma taron jama’a masu murna — wani yanayin biki mara iyaka da ya bambanta da yanayin yaki.
Iraniyawa sun nuna juriya da ƙalubale irin na lokacin yaƙi a wani gagarumin gangami a Tehran
Bayan kwanaki 40 na yakin Amurka da Isra'ila, kasar Iran ta kasance cikin kwanciyar hankali tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 8 ga watan Afrilu. / AP

Iraniyawa sun yi wani biki da ba a saba ganin irinsa ba a daidai lokacin yaƙin Amurka da Isra'ila a kan ƙasar, inda suka ringa tururwa zuwa titunan Tehran don jin daɗin kaɗe-kaɗen ‘yan badujala na sojin Iran, da kuma yin jerin gwanon babura yayin da suke bikin ranar Idin Ghadir na mabiya Shi'a.

A ranar Alhamis, titunan Tehran, waɗanda aka kawata su da balan-balan masu launuka da ƙayatarwa da tutocin Iran, kuma suka cika da masu biki da suka kai tsawon kilomitoci, sun nuna gagarumin yanayin hannun riga da yunƙurin diflomasiyya mai cike da tashin hankali.

Hadi Shabazi, mai shekaru 42, shugaban wata cibiyar ilimi ta yanar gizo, ya ce al’ummar Iran suna “aika sako na karsashi da izza” ta hanyar gudanar da bikin duk da cewa ana tsaka da yaƙi.

Sa’o’i kaɗan kafin a fara bukukuwan, Jagoran Addinin Iran, Mojtaba Khamenei, ya fitar da wata sanarwa a rubuce inda ya yi gargaɗin cewa Isra’ila da Amurka suna ƙoƙarin raba kan Iraniyawa bayan sun fuskanci “babban ƙalubale mai raɗaɗi” a yakin.

Rabiei, wata tsohuwar malama mai shekaru 58 wacce ta ki bayyana sunanta na farko, ta ce ya zama dole Iranawa su fito saboda idan ba su yi hakan ba, “bakar aniyar maƙiya da kwaɗayinsu za su ci gaba da ƙaruwa ne kawai”.

Masu biki da dama sun fito tare da iyalansu, inda wasu matasa suka yi amfani da damar don yin aure.

‘Kada a ja da baya’

Hukumomin Iran sun mayar da bikin ya zama wani babban taro, amma kuma yaƙin yana nan dab da su.

An ajiye wani makami mai linzami na Iran a tsakiyar hanya, inda mazauna yankin suka taru a kusa da shi domin ɗaukar hoto.

“Idan har waɗannan jami’an da gaske suna jin muryar mutane kuma hakan yana da muhimmanci a gare su, to kada su yi sulhu kuma kada su ja da baya a karkashin kowane irin yanayi,” in ji Reyhaneh Ab-Roshan, wata ɗaliba mai shekaru 18.

Hukumomin Iran sun nemi su haɗa sulhu da Amurka da zaluncin da Isra’ila ke yi wa Lebanon.

“Suna bukatar goyon baya, karsashi, da ƙwarin gwiwa, kuma ta wata fuskar suna bukatar goyon bayan al’ummar Iran,” in ji Farid Ahmadi, wani lauya mai shekaru 29.

“Dole ne mu goyi bayansu.”

Amurka ta bi sahun Isra’ila wajen kai wa Iran hari a ranar 28 ga watan Fabrairu, inda hare-haren suka yi kashe Jagoran Addini, Ali Khamenei, da ma sauran manyan jami’an gwamnati da na soji da dama.

Amma Iran ta hanzarta mayar da martani ta hanyar karɓe iko da Tekun Hormuz, wata ƙaramar hanyar ruwa da kashi daya cikin biyar na man fetur din duniya ya taba bi ta cikinta, kuma ta yi ruwan bama-bamai na makaman linzami da jiragen marasa matuƙa a kasashen Larabawa na yankin Tekun Fasa da ke kawance da Amurka, lamarin da ya tarwatsa zaman lafiyar da waɗannan kasashe masu arziki da man fetur suka dade suna taƙama da shi.

Bayan kwanaki 40 ana yakin, Iran ta kasance cikin kwanciyar hankali tun bayan da yarjejeniyar tsagaita wuta da Pakistan ta shiga tsakani ta fara aiki a ranar 8 ga watan Afrilu.

To sai dai tattaunawar da aka yi ta tsawon makonni ta gaza cim ma yarjejeniyar samar da zaman lafiya mai ɗorewa, yayin da ake ci gaba da fuskantar zaman dar-dar tare da yin musayar harbe-harbe lokaci-lokaci, kamar wanda ya faru a wannan makon a Tekun Hormuz, da Kuwait da Bahrain.

Isra’ila da Amurka sun dade suna zargin Iran da son kera makamin kare-dangi na nukiliya, inda Shugaba Trump ya bayyana wannan barazana a matsayin hujja ta kai wa Iran hari.

Trump ya nace kan cewa dole ne Iran ta amince a kowace irin yarjejeniya ta kawo ƙarshen yakin cewa, ba za ta mallaki makamin nukiliya ba, kuma dole ne a lalata sinadarin uranium ɗinta.

Iran ta sha musanta wata aniya ta soja, tana mai jaddada haƙƙinta na mallakar fasahar don amfanin yau da kullum na farar hula.