| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Amurka ta sa takunkumi kan wani ɗan canji dan Nijeriya da wasu kamfanoni kan zargin tallafa wa Daesh
Amurka ta bayyana cewa babban wanda ake zargi da tallafa wa Daesh ɗin ta hanyar canjin kuɗi ɗan Nijeriya ne, yayin da uku daga cikin kamfanoni shida da aka sanyawa takunkumin suke da rassa a Nijeriya, biyu a Jihar Lagos, guda ɗaya kuma a Jihar Kano.
Amurka ta sa takunkumi kan wani ɗan canji dan Nijeriya da wasu kamfanoni kan zargin tallafa wa Daesh
Shugaban Amurka Donald Trump / AP

Ƙasar Amurka ta ƙaƙaba wa wani mutum mazaunin Nijeriya takunkumi, inda ake zarginsa da taimaka wa ƙungiyar Daesh wajen tura kuɗaɗe ta iyakokin ƙasashe daban-daban ta hanyar sana’ar canjin kuɗi.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin, mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, Tommy Pigott, ya bayyana cewa ɗan Nijeriyar yana ɗaya daga cikin mutane uku da kuma kamfanoni guda shida da aka sanya wa takunkumin saboda zargin sauƙaƙa hanyoyin samar da kuɗaɗe ga ƙungiyar Daesh a faɗin yankunan Turai, Gabas Ta Tsakiya, da kuma Yammacin Afirka.

Pigott ya bayyana cewa mutanen da takunkumin ya shafa sun haɗa da wani mai taimaka wa ƙungiyar, mazaunin ƙasar Faransa wanda ake zargi da samar da bayanan abubuwan fashewa ga magoya bayan Daesh, da wani mai gudanar da harkoki mazaunin ƙasar Siriya wanda ake zargi da yin amfani da kuɗaɗen intanet na ‘cryptocurrency’ wajen tura kuɗaɗe ga abokan hulɗar Daesh a ƙasashe da dama, haɗi da Amurka, da kuma wani mai taimaka wa ƙungiyar mazaunin Nijeriya wanda aka yi amfani da sana’arsa ta canjin kuɗi wajen tura kuɗaɗe ga ƙungiyar.

Amurka ta bayyana cewa babban wanda ake zargi da tallafa wa Daesh ɗin ta hanyar canjin kuɗi ɗan Nijeriya ne, yayin da uku daga cikin kamfanoni shida da aka sanyawa takunkumin suke da rassa a Nijeriya, biyu a Jihar Lagos, guda ɗaya kuma a Jihar Kano.

Rumbun Labarai
Netanyahu ya fusata Trump bayan ya caccaki shirin Amurka na sayar wa Turkiyya F-35: Rahoto
Ana fargabar mutuwar 'yan ƙabilar Rohingya fiye da 500 bayan kifewar jiragen ruwa a gaɓar Myanmar
Masu ceton dabbobi na taimaka wa tsuntsaye tsira daga bazara mai zafi
Ƙirkirarriyar Basira, ƙarfin intent da ƙa’idojin aikin jarida
Yawan masu kamuwa da cutar kansa na iya kusan ninkuwa nan da shekarar 2050
Mai tsaron bayan Argentina ya ce alƙalan wasan Gasar Kofin Duniya 'na aiki mai kyau'
An kona gini mai kama da masallaci a Arewacin Ireland  a yayin da ‘yansanda ke gudanar da bincike
An samu rahotannin cin zarafin mata kusan 9,800 a shekarar 2025, fiye da ninki biyu kan na 2024: MDD
Mene ne takunkuman CAATSA kuma ta yaya cire su da Amurka za ta yi zai amfani Turkiyya?
Shugaban Koriya ta Arewa ya je kallon gwajin makami mai linzami mai iya ɗaukar nukiliya
Tafiyar al'ajabin Cape Verde ta ƙare, amma ƙasar Afirkan ta fice daga gasar kofin duniya da suna
TikTok da Youtube sun rufe shafukan yara miliyan 4.7 a Indonesia bayan matakan gwamnati
NATO za ta bayyana biliyoyin daloli a wasu sabbin kwangilolin tsaro a taron Ankara
An ɗaure 'yan Nijeriya sha biyu a Jamus saboda 'zamba ta hanyar soyayya'
Venezuela ta ayyana dokar ta-ɓaci bayan tagwayen girgizar ƙasa, ana fargabar dubbai sun mutu
Tagwayen girgizar ƙasa masu ƙarfi sun afka wa Venezuela, an ba da rahoton ɓarna da yawa
Majalisar Dattijan Amurka ta umarci Trump ya kawo ƙarshen yaƙin Iran
Starmer ya yi murabus daga matsayin Firaministan Birtaniya
Amurka da Iran sun kammala tattaunawa a matakin ƙoli a Switzerland, a cewar masu shiga tsakani
Ɗanwasan film ɗin Breaking Bad Giancarlo Esposito ya karɓi Musulunci a Saudiyya: rahoto