| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Yawan masu kamuwa da cutar kansa na iya kusan ninkuwa nan da shekarar 2050
Haka kuma, yawan masu rayuwa bayan kamuwa da cutar ya fi ƙanƙanta a ƙasashe masu ƙarancin kuɗaɗen shiga idan aka kwatanta da ƙasashe masu arziki.
Yawan masu kamuwa da cutar kansa na iya kusan ninkuwa nan da shekarar 2050
Tsohon hoto: Yawan masu kamuwa da cutar kansa na iya kusan ruɓanya nan da shekarar 2050 / TRT World

Yawan masu kamuwa da cutar kansa a duniya na iya kaiwa kusan miliyan 35 a duk shekara nan da shekarar 2050, matuƙar gwamnatoci ba su ɗauki matakan gaggawa na ƙarfafa rigakafi, faɗaɗa samun kulawar lafiya, da rage gibin da ke akwai wajen samun ingantattun ayyukan kiwon lafiya ba, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO).

A cikin rahotonta na Global Status Report on Cancer 2026, wanda ta fitar tare da Hukumar Bincike kan Cutar Kansa ta Duniya (International Agency for Research on Cancer), WHO ta ce cutar kansa ita ce ta biyu cikin manyan musabbabin mutuwa a duniya bayan cututtukan zuciya da hanyoyin jini, inda take kashe kimanin mutane miliyan 10 a kowace shekara, wato sama da mutum 26,000 a kullum.

Rahoton ya kuma yi gargaɗin cewa gibin da ke akwai wajen kula da masu cutar kansa na ƙara faɗaɗa, saboda damar samun rigakafi, gano cutar da wuri, magani da kuma kulawar bayan magani na bambanta ƙwarai tsakanin ƙasashe.

Haka kuma, yawan masu rayuwa bayan kamuwa da cutar ya fi ƙanƙanta a ƙasashe masu ƙarancin kuɗaɗen shiga idan aka kwatanta da ƙasashe masu arziki.

WHO ta ce cutar kansa na shafar kusan kowa da kowa, inda aka yi hasashen cewa kashi 92 cikin 100 na mutane za su taɓa fuskantar cutar a rayuwarsu, ko dai su kansu su kamu da ita ko kuma wani na kusa da su a cikin iyali.

"Damar mutum ta tsira daga cutar kansa bai kamata ta dogara da inda aka haife shi ko kuma yawan kuɗin da yake samu ba," in ji Babban Daraktan Hukumar Lafiya ta Duniya, Dr. Tedros Adhanom Ghebreyesus.

Rumbun Labarai
Turai na babbakewa: Me muka sani zuwa yanzu?
Faransa da Sifaniya na fama da mummunar gobarar daji
Yadda kujerar Firaministan Birtaniya ke komawa tamkar kujerar aski
Trump ya ce ba za a yi yarjejeniyar nukiliya da Saudiyya ba sai ta amince da gyara alaƙa da Isra'ila
Trump ya tarbi gawawwakin sojojin Amurka da aka kashe a yaƙin Iran
Trump ya amince da yarjejeniyar shirin nukiliya na farar-hula da Saudiyya — Rahoto
Sabon Firaministan Birtaniya Burnham ya yi alƙawarin rage tsadar rayuwa
Netanyahu ya fusata Trump bayan ya caccaki shirin Amurka na sayar wa Turkiyya F-35: Rahoto
Ana fargabar mutuwar 'yan ƙabilar Rohingya fiye da 500 bayan kifewar jiragen ruwa a gaɓar Myanmar
Masu ceton dabbobi na taimaka wa tsuntsaye tsira daga bazara mai zafi
Ƙirkirarriyar Basira, ƙarfin intent da ƙa’idojin aikin jarida
Mai tsaron bayan Argentina ya ce alƙalan wasan Gasar Kofin Duniya 'na aiki mai kyau'
An kona gini mai kama da masallaci a Arewacin Ireland  a yayin da ‘yansanda ke gudanar da bincike
An samu rahotannin cin zarafin mata kusan 9,800 a shekarar 2025, fiye da ninki biyu kan na 2024: MDD
Mene ne takunkuman CAATSA kuma ta yaya cire su da Amurka za ta yi zai amfani Turkiyya?
Shugaban Koriya ta Arewa ya je kallon gwajin makami mai linzami mai iya ɗaukar nukiliya
Tafiyar al'ajabin Cape Verde ta ƙare, amma ƙasar Afirkan ta fice daga gasar kofin duniya da suna
TikTok da Youtube sun rufe shafukan yara miliyan 4.7 a Indonesia bayan matakan gwamnati
NATO za ta bayyana biliyoyin daloli a wasu sabbin kwangilolin tsaro a taron Ankara
An ɗaure 'yan Nijeriya sha biyu a Jamus saboda 'zamba ta hanyar soyayya'