Iran ta sanar da cewa an kai hare-hare kan manyan wuraren soja 18 na Amurka a Kuwait da Bahrain, a yayin da tashin hankali a yankin ke ƙaruwa cikin sauri.
Jami'an Rundunar Juyin Juya Hali (IRGC) na Iran sun ce wuraren da aka nufa sun haɗa da sansanonin Ali Al Salem da Ahmad Al Jaber a Kuwait, tare da sansanin Sheikh Isa a Bahrain.
A wani ɓangare kuma, sojojin Iran sun ce sun kai hari kan tsarin makaman "Patriot" masu kakkaɓo makamai da kuma cibiyoyin sadarwa mallakar Rukunin Jiragen Ruwa na Biyar na Amurka (US Fifth Fleet) a Bahrain.
Sun kuma ƙara da cewa an tura jirage marasa matauƙa masu ƙunar bakin wake zuwa Rukunin Jiragen Ruwa na Biyar a matsayin martani ga abin da suka bayyana a matsayin hare-haren Amurka a kudancin Iran.
Wannan lamari ya faru ne cikin yanayi na ƙaruwa tashin hankali, biyo bayan hare-haren Amurka a kudancin Iran da kuma martanin Iran da ya biyo baya wanda ya nufi kadarorin sojin Amurka a fadin yankin.
Hare-haren da aka saita a fadin Iran
Sabbin tashin-hankalin sun biyo bayan wani sabon jerin hare-haren Amurka kan wurare da dama a Iran, abin da Rundunar Sojin Amurka ta bayyana a matsayin martani ga abin da ta kira "miyagun hare-haren Iran na ba gaira ba dalili”.
Jim kaɗan bayan sanarwar, kamfanin dillancin labarai na gwamanati Mehr ya ruwaito sabbin fashe-fashe a Bandar Abbas da Sirik, da kuma wata fashewa a kusa da Minab a lardin Hormozgan na kudu.
Wadannan hare-haren sun taƙaita ne kan ayyukan soja masu yawa a yankin. Tun da farko a ranar Laraba, Mehr ya ce fashe-fashen da aka ji a wajen birnin Fars sun faru ne sakamakon kunna tsarin kariyar sama.
Haka nan an ji ƙarar makaman harbo jiragen sama a saman yammacin Tehran, yayin da a kusa da tsibirin Kish aka ji wasu fashe-fashe daga nesa.












