| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta dakatar da tattaunawa da Amurka saboda hare-haren Isra'ila a Lebanon: rahoto
Tehran ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawa ba har sai Isra'ila ta daina kai hari a Gaza da Lebanon, kamar yadda kafafen watsa labarai na Iran suka bayyana.
Iran ta dakatar da tattaunawa da Amurka saboda hare-haren Isra'ila a Lebanon: rahoto
Hayaki na tashi a Lebanon bayan wani harin sama, kamar yadda aka gani daga bangaren Isra'ila na kan iyakar Isra'ila da Lebanon. / Reuters

Iran ta dakatar da tattaunawar da take yi da Amurka a matsayin martani kan ci gaba da hare-haren Isra'ila a Lebanon, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya sanar.

A cewar hukumar a ranar Litinin, an yanke wannan shawarar ne a matsayin martani ga abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra'ila ke yi a Lebanon, wanda Iran ke ganin shi ne ɗaya daga cikin sharuɗɗan yarjejeniyoyin tsagaita wuta a yankin.

Tasnim ta ce tawagar tattaunawar Iran za ta dakatar da “hirarraki da musayar rubuce-rubuce ta hanyar masu shiga tsakani” har sai an cika mata buƙatunta dangane da Gaza da Lebanon.

Rahoton ya ce jami'ai da masu tattaunawar Iran sun jaddada buƙatar dakatar ayyukan sojojin Isra’ila cikin gaggawa a Gaza da Lebanon da kuma janyewar duka sojojin Isra'ila daga wuraren da suka mamaye a Lebanon.

“Muddun ba a magance matsalolin Iran da na dakarun gwagwarmaya da ke fagen daga ba, ba za a ci gaba da tattaunawa ba,” in ji Tasnim.

Kamfanin dillancin labaran ya kuma ruwaito cewa Iran da ƙungiyoyinta ƙawaye ‘yan gwagwarmaya sun yanke shawarar shirya mayar da martani ga hare-haren Isra'ila da kuma la'akari da buɗe wasu fagagen yaƙi.

A cewar rahoton, matakan da ake la'akari da su sun haɗa da rufe gaba ɗaya Mashigar Hormuz da buɗe wasu fagagen yaƙi, ciki har da Mashigar Bab al-Mandab, a matsayin hanyar matsa wa Isra'ila da magoya bayanta.