| Hausa
TATTALIN ARZIKI
3 minti karatu
Matatar Dangote ta sayar da hannayen-jarin fiye da naira biliyan 10 mintuna kaɗan bayan ƙaddamarwa
Matatar man fetur ta Dangote da ke Nijeriya ta jawo hankalin masu zuba jari inda suka sayi hannayen-jari na fiye da naira biliyan 10 mintuna kaɗan bayan buɗe sayar da hannayen-jarin ga jama’a a karon farko a ranar Litinin.
Matatar Dangote ta sayar da hannayen-jarin fiye da naira biliyan 10 mintuna kaɗan bayan ƙaddamarwa
Dangote ya buɗe kasuwar hannun-jarin da kuma bikin sayar da shi ga ‘yan kasuwa da misalin ƙarfe 9:35 na safe, agogon ƙasar, a Legas.

Matatar man fetur ta Dangote da ke Nijeriya ta jawo hankalin masu zuba jari inda suka sayi hannayen-jari na fiye da naira biliyan 10 mintuna kaɗan bayan buɗe sayar da hannayen-jarin ga jama’a a karon farko a ranar Litinin, a cewar jami’ai. Ana sa ran cinikin zai iya zama mafi girma na sayar da hannun jari ga jama'a da aka taɓa yi a Afirka.

Aigboje Aig-Imoukhuede, shugaban Access Holdings, ɗaya daga cikin manyan rukunin bankuna a Nijeriya, ya ce dubban masu zuba jari sun yi rajistar neman sayen hannun jarin cikin mintuna kaɗan bayan buɗe cinikin.

“An riga an samu buƙatun sayen hannayen-jari na biliyoyin naira daga dubban masu zuba jari cikin mintuna kaɗan ko ƙasa da awa guda,” in ji Aig-Imoukhuede yayin bikin buɗe cinikin a Nigerian Exchange (NGX) da ke Legas.

Shugaban NGX, Umaru Kwairanga, shi ma ya tabbatar da cewa an riga an yi rajistar buƙatun sayen hannun jari na fiye da naira biliyan 10 tun bayan buɗe cinikin da ƙarfe 8 na safe.

Rukunin farko na sayar da hannayen-jarin ga jama’a wanda aka fi sani da IPO, wanda zai gudana daga ranar 14 ga Satumba zuwa 13 ga Oktoba, na da burin tara dala biliyan 1.6 daga masu zuba jari a faɗin Afirka, tare da burin samun masu hannun jari har miliyan 10. Ana sa ran za a fara cinakayyar hannun-jarin matatar a kasuwar hada-hadar hannayen-jari ta Nijeriya a watan Nuwamba.

A cewar kamfanin, za a yi amfani da kuɗin da aka tara wajen faɗaɗa ƙarfin tace man matatar daga ganga 700,000 na ɗanyen mai a kowace rana a yanzu zuwa ganga miliyan 1.4 a kowace rana nan da shekarar 2030.

Masu AlakaTRT Afrika - Matatar Dangote za ta buɗe sayar da hannayen-jari na Naira tiriliyan 2.15


Matatar, wadda ke kusa da Legas, mallakin hamshakin ɗan kasuwar Nijeriya Aliko Dangote ce, kuma ta fara aiki a shekarar 2024. Idan ta kai cikakken ƙarfin aiki, ana sa ran za ta zama ɗaya daga cikin manyan matatun mai masu tsarin tacewa guda ɗaya a duniya, tare da ƙara ƙarfin Nijeriya na tace ɗanyen man da take haƙowa a cikin gida.

An kiyasta darajar Matatar Dangote a kusan dala biliyan 49 a cikin IPO ɗin. Masu nazari sun ce fara hada-hadar hannun-jarin matatar a kasuwa na iya ƙara jumullar darajar kamfanonin da ake hada-hadarsu a kasuwar hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya da kusan kashi ɗaya bisa uku.

Dangote ya buɗe kasuwar hannun-jarin da kuma bikin sayar da shi ga ‘yan kasuwa da misalin ƙarfe 9:35 na safe, agogon ƙasar, a Legas, tare da manyan jami’an matatar da wakilan wasu cibiyoyin hada-hadar kuɗi na Afirka.