| Hausa
TATTALIN ARZIKI
2 minti karatu
Ƙungiyar EU ta sanar da sanya sabbin takunkumai kan cinikayyar zinare a Sudan
Ƙungiyar Tarayyar Turai ta gabatar da wasu sabbin takunkumai da suka shafi cinikayyar zinare a Sudan da kuma taƙaita damar samun sinadarai da ake amfani da su a haƙar zinare.
Ƙungiyar EU ta sanar da sanya sabbin takunkumai kan cinikayyar zinare a Sudan
"Zinare ya zama babban tushe na samun kuɗin shiga wanda ke ci gaba da rura matsalar tashin hankali a Sudan," a cewar Majalisar Tarayyar Turai,

Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ranar Litinin ta sanya sabbin takunkumai da suka shafi cinikayyar zinare na Sudan da kuma taƙaita damar samun sinadarai da ake amfani da su a haƙar zinare.

Ta ce ta ɗauki matakin ne domin katse kuɗi da ke tallafa wa rikici da tashe-tashen hankula a Sudan da kuma ƙara matsin lamba ga waɗanda ake zargi da rura wutar yaƙin, a cewar wata sanarwa daga Majalisar EU.

A ƙarƙashin matakai dai, ƙungiyar EU ta haramta saye da shigowa da kayayyaki da kuma jigilar zinare daga Sudan, yayin da kuma ta haramta sayarwa, samarwa, canja wuri, da kuma fitar da sinadarin mercury da cyanide a ƙasar.

Kazalika takunkuman sun haɗa da ayyukan da suka shafi samun taimakon fasaha da ayyukan dillalai da tallafin kuɗi da ke da alaƙa da kayayyakin da aka haramta.

Rikicin jinƙai 

"Zinare ya zama babbar hanyar samun kuɗin shiga wanda ke ci gaba da rura matsalar tashin hankali a Sudan," a cewar Majalisar Tarayyar Turai.

Majalisar ta ƙara da cewa, taƙaita kasuwancin zinare a Sudan da kuma samun sinadarai da ake amfani da su wajen haƙar zinare za su rage albarkatun da ke shiga hannun waɗanda ke da alhakin ci gaba da yaƙin da ya dabaibaye Sudan.

Tun a watan Afrilun 2023 ne Sudan ta tsunduma cikin yaƙi, bayan ɓarkewar faɗa a tsakanin sojoji da kuma Rundunar dakarun sa-kai ta (RSF) kan shirin haɗa rundunar cikin sojojin ƙasar.

Yaƙin ya haifar da ɗaya daga cikin rikice-rikicen jinƙai mafiya muni a duniya, inda ya kashe dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu.

Rumbun Labarai
Kayan da Turkiyya ta fitar zuwa Afirka a 2026 sun haura na dala biliyan 13
Kuɗin Ghana ya koma fuskantar matsi, na Uganda na farfaɗowa, na Nijeriya zai iya sauyawa kaɗan
Amurka ta yi barazanar saka wa tattalin arzikin Iran takunkumin da 'duniya ba ta taɓa gani ba'
Gwamnatin Nijeriya za ta farfado da burtalan kiwo 417 a faɗin ƙasar
Za a gyara kamfanin NNPC tare da sayar da hannayen jarinsa a kasuwar hannayen jarin Nijeriya —Tinubu
Matatar Dangote ta fitar da tan fiye da 400,000 na man jiragen sama zuwa Turai a watan Yuli - Rahoto
Hukumar Kasuwanci Marar Shinge ta Afirka ta sanya hannu da wani kamfanin Nijeriya don inganta fito
A lokacin da cututtuka suka tsallaka iyaka: Manoman Afirka na neman sabbin matakan kariya
Farashin fetur a Amurka ya tashi sakamakon tsaiko a Hormuz da sanarwar Houthi ta rufe Bahar Maliya
ECOWAS ta sanya hannu kan yarjejeniyar tallafa wa aikin bututun iskar gas na Nijeriya da Morocco
Hauhawar farashin kayayyaki a Ghana ta ƙaru a wata uku a jere da 5.3% a Yunin 2026
Wa yake amfana a lokacin da tattalin arzikin duniya ke ci da wuta sakamakon yaƙi?
Abubuwan da dalar Amurka Tiriliyan 1.1 mallakin Elon Musk za ta iya yi a Afirka
Elon Musk ya zama tiriloniya na farko a tarihin duniya
An zargi matatar mai mafi girma a Afirka da ƙoƙarin yin babakere game da man Nijeriya
Biliyoyin kudi da gangunan mai: Yadda matatar mai ta Dangote ke ƙarfafar Afirka da makamashi
China ta faɗaɗa janye haraji baki ɗaya ga kayan da ta shigar daga ƙasashen Afirka 53
Wasu daga waje na ƙoƙarin daƙile ci-gaban Afirka, in ji  Dangote
Ghana ta bai wa wani kamfanin ƙasar lasisin haƙar zinare kan $1bn
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi