Rikici ya sake rinceɓewa tsakanin Amurka da Iran, inda Shugaban Amurka Donald Trump ya yi gargadin cewa hare-haren da ake kai wa Iran za su ci gaba da tsananta a cikin kwanaki masu zuwa, yana mai gargadin cewa idan har Tehran ta ki komawa kan teburin tattaunawa, Amurka za ta soma kai hari kan tashoshin wutar lantarki da gadoji na ƙasar a mako mai zuwa, kamar yadda ya bayyana a wata hira da gidan Talabijin na Fox News ta yi da shi.
Kalaman nasa na zuwa ne yayin da ita ma Iran ke zafafa kai hare-hare a cibiyoyin Amurka a Gabas ta Tsakiya.
