| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Iran ta ce lokaci ya yi da Saudiyya za ta kori sojojin Amurka daga yankinta
Babban jami'in diflomasiyyar Iran Abbas Araghchi ya buƙaci Saudiyya da ta kori sojojin Amurka a yankinta bayan harin da aka kai wa wani kamfanin jiragen sama na Amurka a kasar.
Iran ta ce lokaci ya yi da Saudiyya za ta kori sojojin Amurka daga yankinta
Jirgin Amurka kirar E-3 ya lalace a sansanin sojin sama na Yarima Sultan a Saudiyya / Reuters

Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi ya buƙaci Saudiyya da ta kori sojojin Amurka daga yankinta, yana mai jaddada cewa hare-haren da take kai wa yankin sun shafi abokan gabarta ne kawai.

"Iran tana girmama Masarautar Saudiyya kuma tana daukarta a matsayin 'yar’uwarta," kamar yadda Ministan Harkokin Waje Iran Abbas Araghchi ya wallafa a shafin X.

"Ayyukanmu na kai hari, muna yin su ne kan abokan gaba wadanda ba sa girmama Larabawa ko Iraniyawa, kuma ba za su iya samar da wani tsaro ba... Kalli abin da muka yi wa rundunar sojin samansu. Lokaci ya yi da za a kori sojojin Amurka."

Kalaman nasa sun biyo bayan lalata wani jirgin sama mai saukar ungulu da kuma tsarin sarrafa jiragen a wani harin da Iran ta kai kan sansanin sojojin Amurka a Saudiyya.

Hotuna sun nuna yadda aka lalata mafi yawan ɓangaren bayan jirgin saman E-3 Sentry a sansanin sojojin sama na Yarima Sultan, mai nisan kilomita 128 kudu maso gabashin Riyadh.

Kazalika an ji wa wasu sojojin Amurka da dama rauni a harin na ranar Jumma'a, kuma akalla jirgin sama ɗaya ya lalace, kama yadda wanu jami'an Amurka ya tabbatar.

Rumbun Labarai
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya
Falasɗinawa na kaɗa ƙuri'a a zaɓen farko tun bayan yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta ƙaddamar a Gaza
Iran ta ce ba kai-tsaye za a yi tattaunawa a Pakistan don kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra’ila ba
Turkiyya da ƙasashe bakwai sun soki Isra'ila kan keta alfarmar Masallacin Ƙudus
Trump ya fasa kai wa Iran hari da makamin nukiliya
Daraktan IEA ya ce ana asarar gangar mai miliyan 13 kullum saboda rufe Mashigar Hormuz
Amurka ta dakatar da jigilar dala zuwa Iraƙi, amma me ya sa take aika kuɗi zuwa Baghdad?
Trump ya tsawaita tsagaita wutar Iran domin bai wa Tehran ƙarin lokaci na tattaunawa
Vance zai tafi Pakistan ranar Talata domin tattaunawa da Iran  — rahoto
Sojan Isra’ila na shan suka bayan ya lalata mutum-mutumin Yesu a Lebanon
Iran ta kai harin ramuwar gayya kan jiragen Amurka a kan ƙwace jirgin dako: Rahoto
Isra'ilawa da dama sun mamaye Masallacin Ƙudus a ƙarƙashin rakiya da tsaron 'yansanda mai tsanani
Trump ya ce Amurka na yin tattaunawa mai kyau da Iran, ya yi gargaɗi kan rufe Mashigar Hormuz
Hare-haren Iran sun lalata fiye da gidaje 1,000 tare da mayar da su kufai a Tel Aviv - Magajin Gari
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Trump ya ce za a yi amfani da ‘manyan katafilolin tone kasa’ don kwashe sinadarin Uranium daga Iran
Iran ta sanar da bude Mashigar Ruwa ta Hormuz ga dukkan jiragen ruwan duniya
Jakadan Iran a MDD ya bayyana ƙawanyar Amurka a matsayin 'matakin tsangwama'