| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta yi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila bayan Trump ya yi iƙirarin daƙile ƙarfin sojinta
Ƙararrawar gargadin hare-haren sama ta rika yin kara a sassa da dama na arewacin Isra’ila, a cewar gidan talabijin na Channel 12.
Iran ta yi ruwan makamai masu linzami kan Isra’ila bayan Trump ya yi iƙirarin daƙile ƙarfin sojinta
Iran ta kai miyagun hare-hare na makamai masu linzami a Tel Aviv don mayar da martani kan sabbin hare-haren Amurka da Isra'ila a Isfahan / AA

Rahotanni daga tashar ta Channel 12 ta Isra’ila sun bayyana cewa Iran ta harba manyan jerin makamai masu linzami har guda uku zuwa arewacin Isra’ila tun da sanyin safiyar ranar Alhamis.

Ƙararrawar gargaɗi hari ta sama ta riƙa kaɗawa a sassan arewacin Isra’ila yayin da tashar ta ce ana ci gaba da ƙoƙarin kakkaɓo makaman daga sararin samaniya.

Gidan talbijin na gwamnatin Iran ya yi iƙirarin cewa makaman sun isa birnin Haifa mintoci kaɗan bayan kalaman Shugaba Trump na cewa yanzu Iran ba ta na’urorin harba makamai masu yawa.

Tun da farko a ranar Alhamis, a wani jawabi da ya yi ta gidan talbijin daga Fadar White House, Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Iran tana da “ƙalilan” ɗin na’urorin harba makamai da suka rage, inda ya ƙara da cewa ƙarfinta na harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙi “an rage su sosai.”

Hakazalika, Trump ya shaida wa ’yan Amurka cewa yana ganin yaƙin da ake yi da Iran zai ci gaba har zuwa tsawon makonni biyu zuwa uku, amma ya bayyana yaƙinin cewa rikicin yana gab da zuwa ƙarshe.

Masu AlakaTRT Afrika - Trump ya ce Amurka za ta bar Iran cikin makonni 2 zuwa 3

Yankin dai yana cikin hali na fargaba tun bayan da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar da harin ta sama a ranar 28 ga watan Fabrairu, wanda ya zuwa yanzu ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 1,340, ciki har da Jagoran Addini na ƙasar, Ali Khamenei.

Ita ma Iran ta mayar da martani ta hanyar amfani da jiragen marasa matuƙa da makamai masu linzami kan Isra’ila, tare da Jordan, Iraƙi, da kuma ƙasashen Larabawa da ke sansanonin sojin Amurka, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da lalata ababen more rayuwa, sannan ya dagula harkokin kasuwannin duniya da zirga-zirgar jiragen sama.

MAJIYA:Anadolu Agency
Rumbun Labarai
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya
Falasɗinawa na kaɗa ƙuri'a a zaɓen farko tun bayan yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta ƙaddamar a Gaza
Iran ta ce ba kai-tsaye za a yi tattaunawa a Pakistan don kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra’ila ba
Turkiyya da ƙasashe bakwai sun soki Isra'ila kan keta alfarmar Masallacin Ƙudus
Trump ya fasa kai wa Iran hari da makamin nukiliya
Daraktan IEA ya ce ana asarar gangar mai miliyan 13 kullum saboda rufe Mashigar Hormuz
Amurka ta dakatar da jigilar dala zuwa Iraƙi, amma me ya sa take aika kuɗi zuwa Baghdad?
Trump ya tsawaita tsagaita wutar Iran domin bai wa Tehran ƙarin lokaci na tattaunawa
Vance zai tafi Pakistan ranar Talata domin tattaunawa da Iran  — rahoto
Sojan Isra’ila na shan suka bayan ya lalata mutum-mutumin Yesu a Lebanon
Iran ta kai harin ramuwar gayya kan jiragen Amurka a kan ƙwace jirgin dako: Rahoto
Isra'ilawa da dama sun mamaye Masallacin Ƙudus a ƙarƙashin rakiya da tsaron 'yansanda mai tsanani
Trump ya ce Amurka na yin tattaunawa mai kyau da Iran, ya yi gargaɗi kan rufe Mashigar Hormuz
Hare-haren Iran sun lalata fiye da gidaje 1,000 tare da mayar da su kufai a Tel Aviv - Magajin Gari
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Trump ya ce za a yi amfani da ‘manyan katafilolin tone kasa’ don kwashe sinadarin Uranium daga Iran
Iran ta sanar da bude Mashigar Ruwa ta Hormuz ga dukkan jiragen ruwan duniya
Jakadan Iran a MDD ya bayyana ƙawanyar Amurka a matsayin 'matakin tsangwama'