| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Isra’ila ce ummul aba'isin haramtaccen yaƙi da Iran: In ji Erdogan na Turkiyya
Shugaba Erdogan ya yi gargadi kan karuwar rikicin yanki, yana mai cewa Turkiyya na da manufar fita daga kangin ba tare da cutuwa ba kuma da nesanta daga kurar yakin.
Isra’ila ce ummul aba'isin haramtaccen yaƙi da Iran: In ji Erdogan na Turkiyya
Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya halarci taron jam'iyyarsa ta AKP na mako-mako a majalisar dokoki da ke Ankara ranar 1 ga Afrilu, 2026. / AA

Gwamnatin Isra’ila ce mai babban alhakin ‘haramtaccen yakin’ da ake ci gaba da yi kan Iran, in Shugaban Kasar Turkiyya Recep Tayyiip Erdogan.

"Gwamnatin Isra'ila ce ke da alhakin wannan yaƙin da ba ya bisa ƙa'ida, wanda ba wai kawai ya mayar da yankinmu yankin rikici ba, har ma janyo wa dukkan bil'adama wahala a fannin tattalin arziki," in ji Erdogan a ranar Laraba, yayin da yake jawabi a taron 'yan majalisar jam'iyyarsa ta Adalci da Ci Gaba (AK) a babban birnin Ankara.

"Bai kamata a manta da cewa kowane digo na jini da aka zubar a yakin zai tsawaita rayuwar siyasa Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ba," in ji shi.

Erdogan ya ce rikicin da ya fara a ranar 28 ga Fabrairu a yankin ya cika watansa na farko kuma yana ci gaba da ƙaruwa da barazanar da hatsari, ya ƙara da cewa fifikon Turkiyya shi ne ta wuce wannan lokaci mai cike da rikici ba tare da wata illa ba kuma ta ƙuduri aniyar nisantar da ƙasar daga wutar rikicin.

Masu AlakaTRT Afrika - Shugaba Erdogan ya koka da rushewar tsarin tafiyar da duniya da ke aiki bisa doron dokoki

"Daga cikin manyan hatsarin da yankinmu ke fuskanta ba wai kawai tsawaita yaƙin ba ne, har ma da hatsarin rikidewa zuwa faɗaɗar rikicin yanki, yayin da hare-haren ramuwar gayya da ke kai hari kan cibiyoyin makamashi, sufuri, da kayayyakin more rayuwa na fararen hula ke ƙara yawan yiwuwar hakan," in ji shi.

Ya ce Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya halarci wani taro na bangarori hudu a Islamabad tare da takwarorinsa na Saudiyya, Masar, da Pakistan, inda aka tattauna matsalolin da ake fuskanta, sannan aka duba matakan da za a dauka don kawo karshen yakin.

Ya kara da cewa Ministan Tsaron Kasar Turkiyya Yasar Guler da Shugaban Hukumar Leken Asiri ta Kasa (MIT) Ibrahim Kalin, da sauran jami'ai su ma suna yin kokari sosai a fannoni daban-daban.

"Idan akwai ɗan ƙaramin fata na kawo ƙarshen zubar da jini, don kawo karshen yakin da daina zubar da hawaye, da kuma warware matsaloli ta hanyar diflomasiyya, wajibi ne mu kwaci damar aiki fatan," in ji shi.

"Tun farkon yaƙin, matsayin Turkiyya, halinta, da saƙonnin da ta aika wa duniya da yankin sun kasance muryar ɗan adam da tunani mai kyau," in ji shi.

Yaƙi da Iran ba shi zai cika burin zaman lafiya a duniya ba, sai dai ya ma lalata shi, in ji Erdogan, yana mai jaddada cewa diflomasiyya, tattaunawa, da sulhu su ne manyan kayan aiki da ake da su don gujewa wannan rashin jituwa, yana mai jaddada buƙatar neman daidaito maimakon dagewa kan buƙatu masu ƙarfi.

"Fatanmu shi ne a buɗe hanyar zaman lafiya ba tare da ƙarin zubar da jini ba, kuma don haka, za mu ci gaba da yin duk abin da za mu iya, ko da kuwa hakan na nufin sanya kanmu a kan layi," in ji shugaban Turkiyya.

Rumbun Labarai
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya
Falasɗinawa na kaɗa ƙuri'a a zaɓen farko tun bayan yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta ƙaddamar a Gaza
Iran ta ce ba kai-tsaye za a yi tattaunawa a Pakistan don kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra’ila ba
Turkiyya da ƙasashe bakwai sun soki Isra'ila kan keta alfarmar Masallacin Ƙudus
Trump ya fasa kai wa Iran hari da makamin nukiliya
Daraktan IEA ya ce ana asarar gangar mai miliyan 13 kullum saboda rufe Mashigar Hormuz
Amurka ta dakatar da jigilar dala zuwa Iraƙi, amma me ya sa take aika kuɗi zuwa Baghdad?
Trump ya tsawaita tsagaita wutar Iran domin bai wa Tehran ƙarin lokaci na tattaunawa
Vance zai tafi Pakistan ranar Talata domin tattaunawa da Iran  — rahoto
Sojan Isra’ila na shan suka bayan ya lalata mutum-mutumin Yesu a Lebanon
Iran ta kai harin ramuwar gayya kan jiragen Amurka a kan ƙwace jirgin dako: Rahoto
Isra'ilawa da dama sun mamaye Masallacin Ƙudus a ƙarƙashin rakiya da tsaron 'yansanda mai tsanani
Trump ya ce Amurka na yin tattaunawa mai kyau da Iran, ya yi gargaɗi kan rufe Mashigar Hormuz
Hare-haren Iran sun lalata fiye da gidaje 1,000 tare da mayar da su kufai a Tel Aviv - Magajin Gari
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Trump ya ce za a yi amfani da ‘manyan katafilolin tone kasa’ don kwashe sinadarin Uranium daga Iran
Iran ta sanar da bude Mashigar Ruwa ta Hormuz ga dukkan jiragen ruwan duniya
Jakadan Iran a MDD ya bayyana ƙawanyar Amurka a matsayin 'matakin tsangwama'