| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Amurka ta ceto direban jirgin F-15 na biyu da ake nema a Iran — Trump
Sanarwar ta fito ne yayin da Iran ta harba makamai masu linzami da na'urorin jiragen sama marasa matuƙa kan Isra'ila da Kuwait a safiyar Lahadi.
Amurka ta ceto direban jirgin F-15 na biyu da ake nema a Iran — Trump
A ranar Juma'a Iran ta harbo jirgin F-15 na Amurka / Reuters

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce rundunar Amurka ta ceto direban jirgin sama na biyu wanda Iran ta harbo inda ya bayyana ceton a matsayin "daya daga cikin mafi jarumtar ayyukan ceto a tarihin Amurka".

"Wannan jarumin ya kasance a gefen abokan gaba a cikin duwatsu masu haɗari na Iran, ana farautarsa da maƙiya," in ji Trump a shafinsa na Truth Social a ranar Lahadi.

"Ya ji raunuka, amma zai samu lafiya."

"Wannan aikin ceton mai ban mamaki ya zo ne a ƙarin nasarar ceto wani jarumin matukin jirgi, jiya, wanda ba mu tabbatar da shi ba, domin ba ma son jefa aikin ceto n biyo cikin hadari hadari."

Sojan saman shi ne mutum na biyu daga cikin ma'aikatan biyu na jirgin F-15 wanda Iran ta ce, a ranar Juma'a, ta harbo shi.

Sanarwar ta fito ne yayin da Iran ta harba makamai masu linzami da na'urorin jiragen sama marasa matuƙa kan Isra'ila da Kuwait a safiyar Lahadi, kuma rana ɗaya bayan Trump ya ce Iran na da awanni 48 don cim ma yarjejeniya ko ta fuskanci "babban bala’i".

Sojojin Amurka sun bar Iran bayan aikin ceto

Rundunar Sojin Amurka ta ƙaddamar da ayyuka da dama a cikin Iran a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin gano direbobin jirgin waɗanda suka fice daga jirgin bayan Iran ta harbo shi inda sojojin suka tuntuɓi hedkatarsu ta hanyar hanyoyin sadarwarsu.

Jami'ai sun ce an ceto matukin jirgi cikin 'yan awanni bayan an harbo jirgin, yayin da ya ɗauki fiye da rana guda kafin a gano matuƙin na biyu. Ɗaya daga cikin jami’an Amurka ya ce aikin ya haɗa da dakaru na musamman inda suka samu taimakon jiragen sama.

A yayin yunƙurin ceton a ranar Juma'a, dakarun juyin juya hali na Iran sun habo jirgin helikwafta na Amurka duk da cewa jirgin ya tsira.

Rumbun Labarai
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya
Falasɗinawa na kaɗa ƙuri'a a zaɓen farko tun bayan yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta ƙaddamar a Gaza
Iran ta ce ba kai-tsaye za a yi tattaunawa a Pakistan don kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra’ila ba
Turkiyya da ƙasashe bakwai sun soki Isra'ila kan keta alfarmar Masallacin Ƙudus
Trump ya fasa kai wa Iran hari da makamin nukiliya
Daraktan IEA ya ce ana asarar gangar mai miliyan 13 kullum saboda rufe Mashigar Hormuz
Amurka ta dakatar da jigilar dala zuwa Iraƙi, amma me ya sa take aika kuɗi zuwa Baghdad?
Trump ya tsawaita tsagaita wutar Iran domin bai wa Tehran ƙarin lokaci na tattaunawa
Vance zai tafi Pakistan ranar Talata domin tattaunawa da Iran  — rahoto
Sojan Isra’ila na shan suka bayan ya lalata mutum-mutumin Yesu a Lebanon
Iran ta kai harin ramuwar gayya kan jiragen Amurka a kan ƙwace jirgin dako: Rahoto
Isra'ilawa da dama sun mamaye Masallacin Ƙudus a ƙarƙashin rakiya da tsaron 'yansanda mai tsanani
Trump ya ce Amurka na yin tattaunawa mai kyau da Iran, ya yi gargaɗi kan rufe Mashigar Hormuz
Hare-haren Iran sun lalata fiye da gidaje 1,000 tare da mayar da su kufai a Tel Aviv - Magajin Gari
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Trump ya ce za a yi amfani da ‘manyan katafilolin tone kasa’ don kwashe sinadarin Uranium daga Iran
Iran ta sanar da bude Mashigar Ruwa ta Hormuz ga dukkan jiragen ruwan duniya
Jakadan Iran a MDD ya bayyana ƙawanyar Amurka a matsayin 'matakin tsangwama'