| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Tururin nukiliya zai jawo asarar rayuka a manyan biranen ƙasashen Gulf ba Tehran ba: Araghchi
"Isra’ila da Amurka sun jefa bam tashar Bushehr sau huɗu yanzu. Fitar tururin zai kawo asarar rayuka a manyan biranen ƙasashen GCC, ba a Tehran ba,"in ji Abbas Araghchi a rubutun da ya yi a shafinsa na X a ranar Asabar.
Tururin nukiliya zai jawo asarar rayuka a manyan biranen ƙasashen Gulf ba Tehran ba: Araghchi
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi / Reuters

Ministan Harkokin Wajen Iran ya ce "fitar tururin makamashin nukiliya zai kawo ƙarshen rayuka a manyan biranen ƙasashen Gulf ba Tehran ba,” bayan Isra’ila ta kai hari tashar makamashin nukiliya ta Iran ta Bushehr.

“Kun tuna fushin ƙasashen Yamma game da rikice-rikice a kusa da Tashar Makamashin Nukiliya ta Zaporizhzhia a Ukraine?

"Isra’ila da Amurka sun jefa bam tashar Bushehr sau huɗu yanzu. Fitar tururin zai kawo asarar rayuka a manyan biranen ƙasashen GCC, ba a Tehran ba,"in ji Abbas Araghchi a rubutun da ya yi a shafinsa na X a ranar Asabar.

Araghchi ya ce hare-haren kan matatun sinadarai na Iran sun kuma bayyana "ainihin manufofin."

A baya a ranar, hare-haren Amurka da Isra'ila sun sauka kan tashar makamashin nukiliya ta Bushehr a Iran, inda suka kashe mutum ɗaya.

Harin ya zo yayin da tashin hankali a yankin ya ƙaru tun bayan da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da wani farmaki na haɗin gwiwa kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya kashe mutane fiye da 1,340 zuwa yanzu, ciki har da a tsohon jagoran adddini na ƙasar Ali Khamenei.

Tehran ta mayar da martani da harin jiragen sama marasa matuƙa da makamai masu linzami a kan Isra'ila da Jordan da Iraki da ƙasashen Gulf waɗanda suka ba sojojin Amurka masauki.

Rumbun Labarai
Mene ne Tehran ke gabatarwa domin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?
Araghchi ya faɗaɗa zirga-zirgar diflomasiyyar Iran daga Islamabad zuwa Moscow
Sisi na Masar ya yi gargaɗi kan 'ƙoƙarin da ake yi da gangan' na sake zana taswirar Gabas ta Tsakiya
Falasɗinawa na kaɗa ƙuri'a a zaɓen farko tun bayan yaƙin ƙare-dangi da Isra'ila ta ƙaddamar a Gaza
Iran ta ce ba kai-tsaye za a yi tattaunawa a Pakistan don kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Isra’ila ba
Turkiyya da ƙasashe bakwai sun soki Isra'ila kan keta alfarmar Masallacin Ƙudus
Trump ya fasa kai wa Iran hari da makamin nukiliya
Daraktan IEA ya ce ana asarar gangar mai miliyan 13 kullum saboda rufe Mashigar Hormuz
Amurka ta dakatar da jigilar dala zuwa Iraƙi, amma me ya sa take aika kuɗi zuwa Baghdad?
Trump ya tsawaita tsagaita wutar Iran domin bai wa Tehran ƙarin lokaci na tattaunawa
Vance zai tafi Pakistan ranar Talata domin tattaunawa da Iran  — rahoto
Sojan Isra’ila na shan suka bayan ya lalata mutum-mutumin Yesu a Lebanon
Iran ta kai harin ramuwar gayya kan jiragen Amurka a kan ƙwace jirgin dako: Rahoto
Isra'ilawa da dama sun mamaye Masallacin Ƙudus a ƙarƙashin rakiya da tsaron 'yansanda mai tsanani
Trump ya ce Amurka na yin tattaunawa mai kyau da Iran, ya yi gargaɗi kan rufe Mashigar Hormuz
Hare-haren Iran sun lalata fiye da gidaje 1,000 tare da mayar da su kufai a Tel Aviv - Magajin Gari
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Trump ya ce za a yi amfani da ‘manyan katafilolin tone kasa’ don kwashe sinadarin Uranium daga Iran
Iran ta sanar da bude Mashigar Ruwa ta Hormuz ga dukkan jiragen ruwan duniya
Jakadan Iran a MDD ya bayyana ƙawanyar Amurka a matsayin 'matakin tsangwama'