| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta ce Mashigar Teku ta Hormuz a bude take ga duniya, amma a rufe ga maƙiya
Mai bayar da shawara ga Shugaban Addini na Iran Velayati ya bayyana cewa yakin Isra’ila-Amurka zai kawo karshe ne duba ga sharuddan Iran a yayin da Iran din ke ci gaba da rike iko da Mashigar Teku ta Hormuz mai muhimmanci.
Iran ta ce Mashigar Teku ta Hormuz a bude take ga duniya, amma a rufe ga maƙiya
Har yanzu "Kasashen Abokai" na samun damar wuce wa ta mashigar tekun Hormuz, in ji Iran. [File photo] / AA / AA
2 awanni baya

A ranar Alhamis Iran ta bayyana cewa Mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a bude ga jiragen ruwa na duniya amma "a rufe" ga maƙiyanta da sansanoninsu na yankin.

Ali Akbar Velayati, mai ba da shawara ga Jagoran Addini na Iran Mojtaba Khamenei, ya fada a cikin wani jawabi da ya yi a shafin sadarwar yanar gizo na X cewa sakamakon yakin zai dogara ne da sharuddan da Iran za ta gindaya maimakon abin da ya bayyana a matsayin "mafarkin" maƙiyanta.

"Mashigar Hormuz a bude take ga duniya, amma za ta ci gaba da kasancewa a rufe ga maƙiyan mutanen Iran da sansanoninsu a yankin," in ji shi.

Velayati ya kara da cewa yakin zai ƙare bisa ga sharuddan Iran.

"Yaƙin zai ƙare da manufofin Iran da ikonta, ba tare da maye da ruɗani na masu kai hari ba," in ji shi.

Jawabinsa ya zo ne sa'o'i bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana a cikin wani jawabi da aka watsa ta gidan talabijin daga Fadar White House cewa Iran tana da jiragen harba makamai masu linzami "ƙalilan" da suka rage kuma an "rage karfin ikonta na harba makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa."

Trump ya ce yana sa ran yakin zai ci gaba na tsawon wasu makonni biyu zuwa uku amma yana ganin rikicin na gab da zuwa "ƙarshe."

Tehran ta ci gaba da kula da mashigar teku ta Hormuz, wata hanya mai mahimmanci ta jigilar makamashi ga ƙasashen Asia, wanda hakan ya ba jiragen ruwan waɗannan ƙasashen da Iran ke kira "ƙasashe masu aminci" damar wucewa.

Tsaron da ake yi a yankin ya ƙaru tun lokacin da Isra'ila da Amurka suka ƙaddamar da wani hari na haɗin gwiwa kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 1,340, ciki har da Jagoran Addini na wancan lokacin Ali Khamenei.

Iran ta mayar da martani da hare-haren jiragen sama marasa matuƙa da makamai masu linzami da aka kai wa Isra'ila, Jordan, Iraki da ƙasashen Gulf waɗanda ke ɗauke da kadarorin sojojin Amurka, wanda ya haifar da asarar rayuka da lalacewar kayayyakin more rayuwa yayin da yake kawo cikas ga kasuwannin duniya da safarar jiragen sama.