Yaki tsakanin Isra'ila da Amurka kan Iran da martanin Tehran sun jawo ɗagawar farashin kayan abinci biyo bayan ƙarin farashin makamashi da taki, in ji hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma'a.
Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta ce Ƙididdigar Farashin Abinci, wadda ke bayar da bayanai kan sauye-sauyen farashin abinci a kowane wata a farashin ƙasa da ƙasa, ta nuna an samu ƙaruwa da kashi 2.4 cikin 100 a watan Maris idan aka kwatanta da Fabrairu.
Wannan shi ne karo na biyu a jere na tashin farashin, kuma hukumar ta ce babban dalilin shi ne ƙarin farashin makamashi da ke da alaƙa da rikici a Gabas ta Tsakiya.
A cikin ƙididdigar, rukunin man gyaɗa shi ne farashinsa ya fi ɗagawa inda shi ne mafi tsananin tashin farashi, wato kashi 5.1 cikin ɗari fiye da Fabrairu, yayin da farashin man ja ya kai matakin da bai taɓa kaiwa ba tun tsakiyar 2022, sakamakon tasirin tashin farashin mai ɗanyen man fetur, in ji FAO.
Duk da haka, rashin yankewar samar da hatsi ya rage illar wannan tashin farashin, in ji FAO.
“Tashin farashin tun bayan fara rikicin ya kasance a hankali, kuma babban abin da ya jawo shi ne karin farashin mai, in ji babban jami’in tattalin arziƙi a FAO, Maximo Torero, a cikin wata sanarwa.
Amma ya yi gargaɗin cewa idan rikicin ya ci gaba fiye da kwanaki 40 kuma farashin taki ya ci gaba da tashi, “manoma za su kasance cikin zaɓi: su yi noma da ta taki kaɗan ko kuma su yi kaɗan ko kuma su yi noma maras tsada.”
“Wadannan zaɓuka za su shafi amfanin da za a samu a nan gaba kuma za su tsara samar da abinci da farashin kayayyaki na sauran wannan shekara da gaba ɗaya na shekara mai zuwa.”
FAO ta gano cewa tsaikon da ake samu ta hanyoyin jigilar abinci ya ƙara jawo “ƙarin rashin tabbas” ga alkama da masara, in ji FAO.








