Wasannin Afirka: Ire-iren launuka da fannonin wasanni a nahiyar

Wasannin Afirka: Ire-iren launuka da fannonin wasanni a nahiyar

Wasannin Afirka da ke gudana a kasar Ghana sun kunshi wasanni iri daban-daban da al'adu.
Magoya baya sun iso cikin zugarsu don tallafawa kungiyoyin kasarsu. Hoto: AFP  

Daga Kudra Maliro

Ghana ta karbi bakuncin taron gasar wasannin Afirka karo na 13 wanda ke dauke da ƴan wasa kusan 4,000 a fannonin wasanni 29, an soma taron ne daga ranar 8 zuwa 23 ga watan Maris.

Taron wanda kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ke shiryawa a madadin kasashe mambobinta duk bayan shekaru hudu ya wuce wasanni, a cewar shugaban kasar mai masaukin baki Nana Akufo-Addo.

Taron wasannin Afirka sun ƙunshi wasanni iri daban-daban har guda 29. Hoto: Wasu

"Wadannan wasannin za su baje kolin al'adu da basirar wasanni na nahiyar Afirka da kuma banbance- banbancen da ke cikinta," in ji shugaban Ghana a Accra babban birnin kasar inda aka soma wasannin a ranar Juma'ar da ta gabata.

Akwai ƴan wasa da ke wakiltar kasashe daga ko ina daga fadin nahiyar a fannonin wasannin daban-daban.

Wasannin Afirka dama ce ta nuna al'adu. Hoto: Wasu

Daga cikin wasannin akwai na kwando da ƙwallon ƙafa da wasan tennis da kuma ɗaga nauyi da tseren keke da ninkaya da kokawa da dai sauransu.

Wasu daga cikin wadanda suka yi nasara za su damar shiga gasar Olympics za a yi a birnin Paris a 2024, a cewar masu shirya gasar, sannan taron zai samu tallafi daga jami'ai 3,000 da masu aikin sa kai 2,000.

 An gudanar da taron wassanin Afirka karo 13 ne a kasar Ghana. 

A bangaren kwallon kafa, kasashe takwas da ke rukunin maza da suka hada da Ghana mai masaukin baki da Nijeriya da Senegal da Gambia da Kongo da Uganda, Sudan ta Kudu, da kuma Benin ne za su fafata da junansu domin zama zakara a gasar.

Ƴan wasan da suka samu nasara, za su je gasar Olympics ta birnin Paris a 2024. Hoto: Wasu

Ana gudanar da gasar wasannin Afirka ne karo na 13 a biranen Accra da Kumasi da kuma Cape Coast.

TRT Afrika