| Hausa
'Yansandan New York sun kama mutumin da ya yi wa Musulmai barazana da wuka
00:19
Rayuwa
'Yansandan New York sun kama mutumin da ya yi wa Musulmai barazana da wuka
'Yan sandan birnin New York sun kama wani mutum da ya yi wa wasu maza Musulmai huɗu barazana da wuka, yayin da suke fita daga Applebee da ke Brooklyn a daren Lahadi, a cewar Majalisar Hulɗa da Musulumai ta Amurka (CAIR).

"Yayin da mutanen ke fita daga wurin, sun lura da wani mutum zaune kusa da ƙofa yana harar inda suke cikin fushi. Ɗaya daga cikinsu ya gane mutumin daga tarurrukan da suka shafi zanga-zanga a baya, inda aka yi zargin an ga mutumin sanye da tutar Isra'ila yana ihu da furta kalaman wariyar launin fata ciki har da 'Ina ƙin Baƙar fata,'" in ji CAIR a cikin wata sanarwa.

"Bayan ɗan lokaci, mutumin ya yi wa mutanen ihu kan su 'dawo ciki,' sai kuma ya bi su zuwa ƙofa, sannan ya zaro da wuka kusa da ƙofar," in ji sanarwar manema labarai.

Ƙarin Bidiyoyi
Alhazai sun hau Dutsen Arfa
Yadda aka ayyana Pantami a dantakarar gwamnan Gombe a PDP
Ethnosport: Ana bikin wasannin gargajiya na duniya a Istanbul
Kasashe 50 sun shiga atisayen sojin Turkiyya na Fees - 2026
Yadda wata babbar mota ta kwace ta yi ajalin mutum hudu a Gombe
Sharhi kan nasarar cin kofin Premier da Arsenal ta yi
Wadanda suka yi harbe-harbe sun dauki bidiyon harin kai-tsaye
Guguwa ta mayar da sararin samaniyar Najaf a Iraqi ruwan goro
Mece ce cutar Ebola? Ta yayya za a kare kai da kuma shawo kan cutar?
Mun zo Turkiyya don tattauna kan yadda za mu inganta haddace Alkur'ani