"Yayin da mutanen ke fita daga wurin, sun lura da wani mutum zaune kusa da ƙofa yana harar inda suke cikin fushi. Ɗaya daga cikinsu ya gane mutumin daga tarurrukan da suka shafi zanga-zanga a baya, inda aka yi zargin an ga mutumin sanye da tutar Isra'ila yana ihu da furta kalaman wariyar launin fata ciki har da 'Ina ƙin Baƙar fata,'" in ji CAIR a cikin wata sanarwa.
"Bayan ɗan lokaci, mutumin ya yi wa mutanen ihu kan su 'dawo ciki,' sai kuma ya bi su zuwa ƙofa, sannan ya zaro da wuka kusa da ƙofar," in ji sanarwar manema labarai.
