A ranar Talata 26 ga watan Mayun 2026 ne Jam'iyyar PDP a Nijeriya ta ayyana Farfesa Isa Ali Pantami a matsayin ɗantakararta ɗaya tilo 'ba hamayya' na gwamnan Jihar Gombe.
Hakan na zuwa ne bayan da a makon da ya wuce Pantami ya sanar da janyewarsa daga zaben fid da gwani na Jam'iyyar APC mai mulkin kasar, bisa zargin cewa an take dokokin zabe.
