| Hausa
Yadda wata babbar mota ta kwace ta yi ajalin mutum hudu a Gombe
00:30
Yadda wata babbar mota ta kwace ta yi ajalin mutum hudu a Gombe
Ana fargabar wasu mutane sun mutu a Jihar Gombe yayin da wasu da dama suka jikkata bayan wata tirela ɗauke da kaya da aka yi zargin ta samu matsalar birki ta ƙwace ta kutsa cikin shaguna da kan mutane da ke tafiya.

Hatsarin ya faru ne a yankin Mile 3 da ke Gombe a ranar Laraba, yayin da tirelar ke tafiya a kan titin Gombe zuwa Yola.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa direban motar ya yi ƙoƙarin kauce wa haddasa mummunan bala’i ta hanyar karkatar da motar daga hanyar da take bi. Sai dai kuma tirelar ta kutsa cikin wasu motoci, shagunan bakin hanya da kuma mutanen da ke kusa da wurin.

Rahotanni sun nuna cewa mutum bakwai ne tirelar ta buge a lokacin hatsarin, inda aka ce mutum uku sun mutu nan take, yayin da sauran suka samu raunuka daban-daban.

Ƙarin Bidiyoyi
Alhazai sun hau Dutsen Arfa
Yadda aka ayyana Pantami a dantakarar gwamnan Gombe a PDP
Ethnosport: Ana bikin wasannin gargajiya na duniya a Istanbul
Kasashe 50 sun shiga atisayen sojin Turkiyya na Fees - 2026
'Yansandan New York sun kama mutumin da ya yi wa Musulmai barazana da wuka
Sharhi kan nasarar cin kofin Premier da Arsenal ta yi
Wadanda suka yi harbe-harbe sun dauki bidiyon harin kai-tsaye
Guguwa ta mayar da sararin samaniyar Najaf a Iraqi ruwan goro
Mece ce cutar Ebola? Ta yayya za a kare kai da kuma shawo kan cutar?
Mun zo Turkiyya don tattauna kan yadda za mu inganta haddace Alkur'ani