"Za a yi amfani da duk dabarun da suka dace wajen kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su," a cewar Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan. / Hoto: Reuters

Jami'an tsaro a yankin kudu maso yammacin Pakistan sun bazama neman 'yan wasan kwallon kafa shida da aka sace a makon jiya, a cewar ministan harkokin cikin gida na kasar.

An sace 'yan wasan ne a garin Sui da ke gundumar Dera Bugti na lardin Balochistan a kan hanyarsu ta zuwa gasar kwallon kafa ta cikin gida.

"An killace yankin gaba dayansa", a cewar sanarwar da Ministan harkokin cikin gida Sarfaz Bugti ya fitar a yammacin ranar Lahadi.

"Za a yi amfani da duk dabarun da suka dace wajen kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su," a cewar Ministan.

Lardin Balochistan mai arzikin albarkatun kasa, ya kasance yanki mafi girma da kuma karancin jama'a a Pakistan, ya kuma shafe shekaru da dama yana fama da tashe-tashen hankula.

TRT World
Muna amfani da ka’idojin yanar gizo. Muna son ku san cewa idan kuka ci gaba da amfani da wannan shafin, kun amince da wadannan ka’idojin.Ka’idoji
Na amince