Ta jadada tsananin al'amarin, inda ta yi nuni da cewa, ana kyautata zaton yara 4,000 suke maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa ko kuma sun ɓata. / Photo: AA

Gaza ta zama "gidan marayu mafi girma a duniya a duniya kuma makabarta mafi girma ga yara a ƙarƙashin ƙasa," in ji uwargidan shugaban kasar Turkiyya Emine Erdogan.

Uwargidan Erdogan a ranar Talata ta bayyana mummunan yanayin da yara kanana ke fuskanta a Gaza a jawabinta na Ranar Kare Iyali, tare da yin tir da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa. Ta bukaci hadin kan duniya don karewa da tallafawa masu rauni.

Ta ce akwai akalla yara 17,000 da ke watangaririya ba tare da iyalansu ba a Gaza kuma ba su da inda za su je.

"A yau, abin takaici ne cewa a sassa daban-daban na duniya, yara suna rayuwa a cikin munanan yanayi, suna fafitikar rayuwa, balle a ce suna da damar rayuwa cikin jin dadi ta iyalai," in ji Erdogan.

Ta jadada tsananin al'amarin, inda ta yi nuni da cewa, ana kyautata zaton yara 4,000 suke maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa ko kuma sun ɓata.

Erdogan ta ce yaran Falasdinawan da Isra'ila ta yi musu ta'asar da babu wani lamiri da zai goyi bayan hakan, an yi musu da tabon da ba zai warke ba .

Akalla Falasdinawa 37,900 galibi mata da yara ne aka kashe yayin da 87,060 suka jikkata a Gaza tun lokacin da Tel Aviv ta kaddamar da farmaki a ranar 7 ga Oktoba, a cewar jami’an kiwon lafiya na yankin.

Fiye da watanni takwas da hare-haren Isra'ila, manyan yankunan Gaza sun zama kufai, a cikin yanayi na takunkuman hana shigar mata da abinci da ruwan sha da magunguna.

TRT World