Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya yi kira ga dukkan kasashen yankin da su goyi bayan kasar Lebanon kan shirin mamayar da Isra'ila ke son yi. /Hoto: AA

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya yi kira ga dukkan kasashen yankin da su goyi bayan kasar Lebanon kan shirin mamayar da Isra'ila ke son yi.

A wani jawabi da ya yi wa kungiyar 'yan majalisar dokoki ta jam'iyyarsa ta Justice and Development Party (AK) a Ankara babban birnin kasar a ranar Laraba, Erdogan ya ce: "Isra'ila da ta lalata Gaza, yanzu ta sanya ido kan Labanon. Mun ga cewa Ƙasashen Yamma suna goyon bayan Isra'ila Ta bayan fage."

"Turkiyya na tsayawa tsayin daka tare da 'yan'uwanta al'ummar kasar Lebanon, kuma ina gayyatar sauran kasashen yankin da su tsaya tsayin daka da Lebanon," in ji Erdogan.

"Shirye-shiryen Netanyahu na yada yaƙin a fadin yankin zai haifar da wani babban bala'i," in ji shi, ya kara da cewa: "Duniyar Musulunci da kasashen Gabas ta Tsakiya ya kamata su zama na farko da za su mayar da martani kan wadannan tsare-tsare na zubar da jini."

Shugaban ya ƙara da cewa, "Abin takaici ne, abin takaici ne cewa ƙasashe, waɗanda ke magana kan 'yanci da 'yancin ɗan'adam, da adalci da mahaukata kamar Netanyahu ke tsare da su."

Ƙudurin UNSC na tsagaita wuta

Isra'ila, wadda ta yi fatali da ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya bukaci a tsagaita wuta cikin gaggawa, ta fuskanci tofin Allah tsine a tsakanin kasashen duniya a daidai lokacin da take ci gaba da kai munanan hare-hare a Gaza tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba.

Kimanin Falasdinawa 37,700 aka kashe tun daga lokacin a Gaza, yawancinsu mata da yara, yayin da wasu fiye da 86,200 suka jikkata, a cewar hukumomin lafiya na yankin.

Fiye da watanni takwas da yakin Isra'ila, manyan yankunan Gaza sun zama kufai sakamakon sanya mata takunkuman shigar da abinci da ruwan sha da magunguna.

Ana tuhumar Isra'ila da kisan kiyashi a kotun kasa da kasa, inda hukuncin da aka yanke na baya-bayan nan ya ba da umarnin dakatar da kai hare-haren soji a kudancin birnin Rafah, inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka daga yakin kafin a mamaye shi a ranar 6 ga watan Mayu.

TRT Afrika