Faduwar Nijeria a teburin FIFA ba za ta rasa nasaba da yadda ta sha kaye a hannun Guinea-Bissau a Abuja ba/ PHOTO:Twitter/Super Eagles

Tawagar kwallon kafar Nijeriya, Super Eagles, ta fadi daga matsayi na 35 zuwa na 40 a sabon teburin da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta fitar.

FIFA ta wallafa bayani kan sabon teburin ne a shafinta na intanet ranar Alhamis.

Kazalika tawagar ta Nijeriya ta yi kasa zuwa mataki na shida a nahiyar Afirka.

Sabon teburin ya nuna kasashe da kuma matsayinsu bisa iya murrza ledarsu.

Jadawalin ya nuna cewa Ajentina ce kasa ta daya a duniya a fagen tamaula yayin da kasar Faransa take biye da ita.

Kasar Morocco da ta kai wasan kusa da na karshe a gasar Kofin Duniya ke kan gaba a Afirka kuma tana ta 11 a duniya.

Kasar Senegal dage rike da Kofin Afrika ce ta biyu a nahiyar yayin da take ta 18 a duniya.

Kasar Guinea-Bissau da ta doke Nijeriya a Abuja ta kara matsawa sama a teburin na FIFA inda ta koma ta 113/Photo: Anadolu

Ita kuma kasar Tunisiya ta koma ta uku a Afrika yayin da take ta 18 a duniya.