Wata sanarwa da Rundunar Sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na X ta bayyana cewa, dakarun sun ci gaba da yin dannawa, domin share hanyar da 'yan ta'addan ke bi wajen tserewa, inda suka mamaye yankin tare da gudanar da ƙarin bincike.
Dukkan mutanen da aka ceto, da motoci da kayayyakin da aka ƙwato an kai su garin Buratai cikin ƙoshin lafiya da aminci.
A halin yanzu ana yi wa fararen hulan da aka ceto rajista da kuma gwaje-gwajen lafiya, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
