| Hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da kashe ‘yanta'adda 1,500 da kubutar da mutane 777 a watanni biyu
A wasu farmakan soji da suka kai, dakarun Nijeriya sun hallaka ‘yanta’adda 1,487, tare da kubutar da mutane 777 da aka yi garkuwa da su a watannin Yuli da Agusta, in ji Hedikwatar Tsaron ƙasar a ranar Talata.
Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da kashe ‘yanta'adda 1,500 da kubutar da mutane 777 a watanni biyu
Nijeriya na fama da matsalolin 'yan ta'adda da masu garkuwa da mutane.

Hedikwatar Tsaron Nijeriya ta ce dakarunta sun ‘yanta’adda 1,487, an kama mutane 354, tare da kubutar da mutane 777 da aka yi garkuwa da su a watannin Yuli da Agusta.

Kakakin Hedikwatar Tsaron Manjo Janar Samaila Uba ne ya bayyana alkaluman a lokacin wani taron manema labarai na tsaro a Cibiyar Yaƙi da Ta'addanci ta Ƙasa da ke Abuja.

Uba ya ce sojoji sun kai farmakai 7,062 da suka shafi ta'addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, da hare-hare kan al'ummomi a cikin watanni biyu.

"An kashe jimillar 'yan ta'adda da masu tayar da kayar baya 1,487, an kama mutane 354, yayin da aka ceto mutane 777 da aka yi garkuwa da su cikin nasara," in ji Uba.

Ya ce an kai farmakan a jihohi da dama, ciki har da Borno, Yobe, Taraba, Katsina, Kwara, Zamfara, Sokoto, Plateau, Benue, Niger, Oyo, da Kaduna.

Sojojin sun ce farmakan sun haɗa da ta ƙasa, sama da ruwa, inda sojoji suka kai farmakan kakkabe ‘yan ta’adda, hare-hare bayan samun bayanai daga ayyukan leƙen asiri, ayyukan ceto da kuma kama mutane da ake nema.

Uba ya ce an kashe jami'an tsaro 93 da fararen hula 249 a yayin farmakan.

Sojoji sun kuma sami bindigogi 991 da harsasai 1,331, yayin da aka gano wasu abubuwan fashewa, kuma aka lalata su cikin nasara.

Kakakin rundunar sojin ya ce sojoji sun kashe mayakan Boko Haram da ISWAP 309 a yayin kai farmakan yaki da ta'addanci, sannan suka kwato abubuwan fashewa guda 44.

An kuma wargaza sansanonin 'yan ta'adda da dama, yayin da aka kwato makamai, babura da dabbobi a lokacin kai farmakan.

Uba ya danganta sakamakon da aikin hadin gwiwa na sojoji, hadin gwiwa tsakanin hukumomi da kuma goyon bayan al'ummomin yankin. Ya bukaci 'yan Najeriya da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanan sirri kan lokaci domin taimakawa ayyukan.

Najeriya ta yi fama da rikicin tsaro na dogon lokaci wanda ya shafi 'yan tawaye, 'yan fashi da makami da kuma garkuwa da mutane, musamman a yankunan arewa maso gabashin kasar.

Rikicin Boko Haram, wanda ta fara a arewa maso gabashin kasar a shekarar 2009, ya ci gaba da girmama, inda ISWAP ta bayyana a matsayin wata babbar kungiyar masu dauke da makamai da ke aiki a yankin.

A cikin 'yan shekarun nan, kungiyoyin 'yan fashi da makami da kuma kungiyoyin masu aikata laifuka sun kuma faɗaɗa ayyukansu zuwa sassan arewa maso yamma da arewa ta tsakiyar Najeriya, suna yin garkuwa da mutane da kai hare-hare kan al'ummomin karkara.

Uba ya bukaci kafafen watsa labarai da su goyi bayan kokarin samar da tsaro ta hanyar bayar da rahotanni masu inganci, na gaskiya da kuma sauke nauyi.