| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Tebboune ya sake bayyana goyon bayan Aljeriya ga Nijar yayin da ake fuskantar barazanar tsaro
Jiragen sojojin Aljeriya huɗu sun isa Yamai yayin da sojojin Nijar suka yi ƙoƙarin ƙwato iko wani wuri mai muhimmanci da aka kai wa farmaki a hare-haren da suka faru a babban birnin ƙasar.
Tebboune ya sake bayyana goyon bayan Aljeriya ga Nijar yayin da ake fuskantar barazanar tsaro
Shugaba Abdelmadjid Tebboune ya sake jaddada wa Abdourahamane Tiani na Nijar goyon bayan Aljeriya 'a kowane irin yanayi'.

Shugaban Aljeriya Abdelmadjid Tebboune ya sake jaddada goyon bayan ƙasarsa ga Nijar, al'ummarta da cibiyoyinta bayan wani yunƙuri na dagula lamura a ƙasar ta Yammacin Afirka.

Tebboune ya yi wannan furucin ne a ranar Litinin a lokacin da ya yi waya da shugaban Nijar Abdourahamane Tiani don tattauna halin da ƙasar ke ciki, a cewar wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar Aljeriya ta fitar.

"Shugaban ya sake tabbatar wa ɗan'uwansa Abdourahamane Tiani cewa Aljeriya za ta ci gaba da goyon bayan 'yar'uwarta Nijar, da al'ummarta da cibiyoyinta, kuma za ta tallafa mata a dukkan fannoni da kuma a kowane yanayi," in ji sanarwar.

Tebboune ya kuma taya Tiani murna kan ƙoƙarinsa wanda ya "kawar da yunƙurin dagula lamura a Nijar."

‘An shawo kan lamarin baki ɗaya’

Tiani, a nasa ɓangaren, ya tabbatar wa Tebboune cewa an "shawo kan lamarin baki ɗaya" kuma ya gode wa Aljeriya saboda tsayawa tare da Nijar da al'ummarta, a cewar sanarwar.

A ranar Lahadi, Ma'aikatar Tsaro ta Aljeriya ta sanar da cewa jiragen saman soja guda huɗu na Algeria sun isa Yamai "a kan wani aiki na tallafa wa sojojin Nijar wajen tunkarar yunƙurin wargaza ƙasar."

Rikicin da ya ɓarke kwanan nan ya haɗa da hare-hare a kusa da filin jirgin saman Diori Hamani da kuma sansanin sojojin sama na 101, wani sansanin sojoji mai mahimmanci a Yamai, da kuma wasu wurare a babban birnin.

Ministan tsaron Nijar ya ce an shawo kan ayyukan soji a Yamai kuma jami'an tsaro sun sake ƙwace iko da muhimman wurare da aka kai hari.