An sako mutane aƙalla 176 da aka yi garkuwa da su lokacin harin ‘yanta’adda na ranar 3 ga Fabrairu a garuruwan Woro da Nuku da ke Karamar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara, tsakiyar Najeriya, abin da ya kawo ƙarshen kusan watanni shida da suka shafe ana tsare da su.
Gwamnatin Jihar Kwara ce ta sanar da hakan a ranar Laraba ta shafinta na Facebook. Ta bayyana sako su a matsayin wata babbar nasara, tare da yaba wa Shugaban ƙasar ta Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, da jami’an tsaro, da duk wanda ya bayar da gudummawa wajen wannan aiki.
“Alhamdulillah muna jinjina ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu GCFR, da jami’an tsaro, da kowane mutum da ya taka rawa a wannan babbar nasara. Muna godiya!” inji gwamnatin.
Duk da cewa har kawo yanzu hukumomi ba su bayyana cikakkun bayanai kan yadda aikin ya gudana ba, majiyoyi da dama daga al’ummar yankin sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa jami’an tsaro, tare da goyon bayan kayan aikin soji, sun shiga cikin daji tun da safiyar ranar kafin labarin ‘yantar da mutanen ya isa ga al’ummomin.
Daily Trust ta rawaito Aliyu Umar, wani mazaunin yankin kuma mamba a tawagar tattaunawa ta al’umma ta hanyar wani mai shiga tsakani, yana cewa rahotannin da ke zuwa ga al’ummomin sun nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani aikin ceto. Ya ce mazauna yankin Wawa da ke kusa da wajen sun ba da rahoton cewa sun ga manyan motoci bakwai ko takwas tare da rakiyar tankokin yaƙi na Sojoji suna shiga cikin daji.
Ya ƙara da cewa bayanan da ke yawo a cikin al’ummomin sun nuna cewa an miƙa waɗanda aka yi garkuwar da su ga jami’an gwamnati. A cewarsa, mazauna yankin sun ba da rahoton ganin motocin bas, da motocin masu ɗauke da bindigogin soja da sauran motocin tsaro na nufar yankin.
“Ba mu yi magana da waɗanda abin ya shafa da kanmu ba a lokacin, amma duk abin da muke ji ya nuna cewa an miƙa su ga tawagar ceto,” in ji shi.
Sakin nasu na nuna wani babban sauyi bayan watanni na rashin tabbas wanda ya haifar da zanga-zanga, da roko, da kuma tattaunawa daga iyalan da abin ya shafa. Wannan sabon ci-gaban ya zo ne kwanaki biyar kacal bayan da iyalai suka bayyana cewa ‘yanta’addan sun ƙi amincewa da kuɗi sama da Naira miliyan 155 da aka tara daƙyar ta hanyar gudummawar al’umma, da tari, da kuma siyar da abubuwa masu daraja.
An yi garkuwa da mutum 176 ne a lokacin wani harin ‘yanta’adda da aka kai garuruwan Woro da al’ummar Nuku a ranar 3 ga Fabrairu, wani hari da ya yi ajalin ɗaruruwan mutane, ya raba iyalai da dama da muhallansu tare da lalata gidaje da ababen more rayuwa na jama’a.
Kisan kiyashin ya haifar da bacin rai a fadin kasar kuma ya sa Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin kara tura dakarun soji da kuma karfafa ayyukan tsaro a Kaiama da yankunan da ke kusa.


















