Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
AFIRKA
7 minti karatu
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasaTa hanyar tura baƙin-haure zuwa wasu ƙasashe da ba nasu ba a Afirka, Amurka na sake fasalin yadda tsarin kula da baƙi a ƙasar zai kasnace. Abin da ake yi na kula da gudun hijira, abu ne da ƙwararru suka kira mayarwa da wasu wahalhalun Amurka.
Ghana ta ce ta karbi bakin haure da aka kora daga Amurka don nuna kishin Afirka. / Reuters
2 awanni baya

Gwamnatin Shugaban Amurka Donald Trump ta sake tayar da muhawara kan korar baƙin-haure zuwa ƙasashen da ba nasu ba - daga ciki wasu ƙasashen Afirka ne.

A farkon watan Afrilu, an tura wasu da aka kora daga Amurka su 12 zuwa Uganda, wanda hakan ya ƙara yawan jerin waɗanda za a tura a faɗin nahiyar. A farkon shekarar, an tura wasu 17 zuwa Kamaru. A shekarar 2025, an mayar da wasu da ba su da yawa zuwa Rwanda (7), Ghana (14), da Sudan ta Kudu (8), yayin da Eswatini ta kaɓbi aƙalla baƙin-haure 19 tsakanin 2025 da 2026.

Duk da haka, wannan matakin ya rufe wani babban buri. Hukumomin Amurka sun bayar da rahoton cewa sun bayar da umarnin korar dubban baƙin-haure zuwa ƙasashen da ba nasu na asali ba a duk duniya, yayin da yarjejeniyoyin ƙasashen biyu da ƙasashen Afirka suka bayyana karfin da za a iya bai wa ɗaruruwan karin baƙin-haure.

Ga masu sharhi, ma'anar a bayyane take: wannan ba manufa ce mara girma ba—tsari ne mai tasowa.

Masana harkokin gudun hijira sun kira wannan da "fitarwa waje": sauya wa 'yan ci-rani waje zuwa ƙasashen da ba nasu ba, galibi nesa da inda suka nemi mafaka.

"Fitarwa waje ba wai kawai game da shawo kan gudun hijira ba ne; ya ma shafi mayar da alhaki kan wasu daban ta hanyoyin da ke nuna tsarin iko na duniya," Therence Atabong Njuafac, ƙwararre a fannin hulɗa da ƙasashen duniya da kimiyyar siyasa ya fada wa TRT Afrika.

Siyasar Karfin Iko

A taƙaice, manufar tana son hana ƙaura da kuma shawo kan ‘yan gudun hijira. Ta hanyar mayar da baƙi zuwa yankuna masu nisa, hukumomin Amurka na da nufin hana shiga kasar ba bisa ƙa'ida ba yayin da suke rage matsin lamba ga tsarin cikin gida.

Amma ga masu lura da mutane da yawa, wannan ba tsari mai kyau ba ne - siyasa ce.

"Batun tura mutum wajen da ba wai gidansa ba ne, har ma zuwa wani yanki da ba a sani ba, yana sanya damuwa a cikin tunani," Njuafac ya fada.

"Tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro yana aiki a alamance kamar yadda yake a zahiri - yana aika saƙo game da sakamakon gudun hijira."

Hanyar ta yi amfani a Tarayyar Turai, inda ake ƙara tura ikon sarrafa gudun hijira zuwa ga ƙasashe a Afirka da Gabas ta Tsakiya.

Ga masu suka, wannan yana nuna haɗewa mai tayar da hankali: ƙasashe masu arziki suna ƙarfafa iyakokinsu ta hanyar aike wa da nauyi da hatsari zuwa ga ƙasashe marasa ƙarfi.

Kora ko raba su da matsugunansu?

Waɗanda waɗannan manufofi suka shafa galibi suna cikin waɗanda suka fi rauni: masu neman mafaka da aka ƙi amincewa da su, baƙi marasa takardu, da kuma mutanen da ƙasashensu ba su da yarjejeniyar mayar da su gida da Washington.

Duk da haka, ɗaya daga cikin batutuwan da suka fi tayar da hankali shi ne inda za su ƙarkare.

A wasu lokuta, ana iya aika waɗanda aka kora zuwa ƙasashen Afirka waɗanda ba su da alaƙa ta sirri, al'adu, ko harshe. Ga Njuafac, wannan yana haifar da damuwa sosai.

"Lokacin da aka aika mutane zuwa ƙasashen da ba su da wata alaƙa mai ma'ana da su, muna fuskantar hatsarin haifar da nau'ikan rashin ƙasa baki daya," in ji shi.

Irin waɗannan yanayi sun ɓata alakar da ke tsakanin kora da gudun hijira, suna barin mutane cikin rikici na shari'a da zamantakewa.

Ga ƙasashen Afirka, wannan yana haifar da tambayoyi masu wahala: Waɗanne wajibai ne ke akwai ga waɗanda ba 'yan ƙasa ba da aka sanya ta hanyar yarjejeniyoyi na kasashen waje? Kuma a wane lokaci ne haɗin gwiwa ya zama tilas?

Sauya iyakoki, dora nauye-nauye

Daga mahangar Amurka, fa'idodin sun a bayyane suke a sarari: ƙarancin shari'o'in da ke makalewa a kotunan shige da fice, rage farashin tsare mutane, da aiwatar da ayyuka a bayyane waɗanda ke ɗauke da alhakin siyasa. Waɗannan shirye-shiryen kuma na iya ƙarfafa dangantakar diflomasiyya, galibi suna da alaƙa da shirye-shiryen taimako ko haɗin gwiwar tsaro.

Duk da haka, Njuafac ya yi gargaɗi game da kallon waɗannan nasarorin a ware.

"Inganci na ɗan gajeren lokaci sau da yawa ya kan janyo illolin shari'a da ɗabi'a na dogon lokaci," in ji shi.

'Yan gudun hijirar da Amurka ta kora zuwa Sudan ta Kudu

Ga ƙasashen Afirka masu karɓar baƙi, yanayin ya fi zama mai rikitarwa.

Wasu gwamnatoci na iya maraba da ƙarfafa gwiwa na kuɗi ko kuma kusanci da Washington. Amma waɗannan fa'idojin suna zuwa da manyan canje-canje. Rashin tsarin cibiyoyi na iya yin wahala wajen ɗaukar sabbin masu shigo wa, yayin da al'ummomin gida na iya yin adawa da matsugunan baƙi waɗanda ba 'yan asalin ƙasar ba.

Har ila yau, akwai damuwa game da tsaro, musamman idan waɗanda aka kora sun haɗa da mutanen da ke da tarihin aikata laifuka.

"Wannan aikin na iya kama da canja nauyin da ke kan wani daga ƙasa mai ƙarfi zuwa wadda ke da rauni a tsarinta," in ji ƙwararren masanin hulɗa da ƙasashen duniya.

Matsalolin shari’a

Bayan kayan aiki da siyasa akwai wata matsala babba ta shari'a.

Dokar kare hakkin dan adam ta duniya—wanda aka gina bisa ka'idoji kamar rashin mayar da 'yan gudun hijira da 'yancin neman mafaka—ta sanya iyaka kan yadda kasashe za su iya kula da bakin haure.

Duk da cewa aika ‘yan gudun hijira na wasu kasashe zuwa kasashen da ba nasu bai saba doka ba, to amma sun dogara ne da tsauraran matakan kariya: aminci, samun hanyoyin neman mafaka, da kariya daga cutarwa.

A zahiri, waɗannan ba koyaushe ake tabbatar da su ba.

"Amincewar da ke cikin waɗannan yarjejeniyoyi galibi ana tsara ta ne ta hanyar rashin daidaiton dangantaka tsakanin karfin kasashe, wanda ke haifar da shakku game da yadda irin waɗannan haɗin gwiwa suke da son rai," in ji Njuafac.

Wannan rashin daidaito yana haifar da tambayoyi marasa daɗi game da ko irin waɗannan manufofin suna wakiltar haɗin gwiwa na gaske - ko kuma kawai fitar da alhaki ne zuwa ga wasu.

Ga ƙasashen Afirka, tasiri nr na yanzu-yanzu kuma ana iya ganin sa.

Gwamnatoci na iya fuskantar matsin lamba kan tsarin gudanarwa da aka riga aka iyakance. Al'ummomi na iya nuna tirjiya game da matsugunan d aka ba wa baki da ba ‘yan kasa ba. Damuwa game da tsaro, haɗin kai, da rarraba albarkatu na iya ƙara faɗaɗa cikin sauri zuwa tashin hankali na zamantakewa.

A lokaci guda kuma, alƙawarin ƙarfafa tattalin arziki na iya sanya gwamnatoci cikin mawuyacin hali—daidaita kwanciyar hankali a cikin gida da haɗin gwiwa da ƙasashen duniya.

Idan irin waɗannan manufofi suka zama daidai, suna fuskantar hatsarin sake fasalin tsarin gudun hijira na duniya ta hanyoyin da ke shafar Kudancin Duniya ba tare da daidaito ba.

Ga masu suka, wannan ba wai kawai game da gudun hijirar ba ne— sukan na zuwa ne game da batun adalci. Suna gargaɗin cewa wannan zai iya daidaita tsarin da ƙasashe masu arziki ke ƙara matsa lamba ga yin gudun hijira zuwa ƙasashe marasa wadata, yana ƙara zurfafa rashin daidaito a duniya a cikin wannan tsari.

"Idan aka yi amfani da su sosai, irin waɗannan manufofi za su iya sake fasalin tsarin mafaka na duniya—ba lallai ba ne ta hanyoyin da ke inganta kariya," in ji Njuafac.

Sake fasalin nauyin da ya rataya a kan kasashe

Muhawarar da ake yi kan korar mutane zuwa Afirka a ƙarshe ta haifar da wata tambaya mai zurfi: wa ke da alhakin kare mafi rauni a duniya?

Ga Amurka, wannan na iya bayar da sassaucin gudanarwa da kuma fahimtar siyasa. Amma ga ƙasashe masu karɓar baƙin - da kuma ga bakin haure su kansu - yana haifar da rashin tabbas, damuwa, da hatsari.

Ba tare da gaskiya ba, kariya mai ƙarfi, da haɗin gwiwa mafi daidaito, "to akwai hatsarin ƙarfafa rashin daidaito a duniya da kuma lalata ƙa'idojin ƙasa da ƙasa kan gudun hijira da haƙƙin ɗan adam," Njuafac ya faɗa wa TRT Afrika.

A yanzu, tambayar ita ce: wajen ƙara tsaurara rufe iyakokinta, shin Amurka za ta sake fasalta su gaba ɗaya?