Aƙalla mutum 23 sun mutu daga annobar da ake ganin ta mashaƙo ce a jihar Filato da ke tsakiyar Nijeriya yayin da cutar mai yaɗuwa ke ci gaba da yaɗuwa a ƙarin wurare, kamar yadda hukumomin tsaro suka bayyana.
Kawo yanzu an samu waɗanda ake ganin cutar ta kama da adadinsu ya kai 143 a yankunan da lamarin ya shafa, in ji jami’an lafiyar gwamnati.
Kwamishinan lafiya na jihar Filato Nicholas Baamlong ya bayyana ranar Talata cewa gwamnatin ta zafafa ƙoƙarin daƙile yaɗuwar cutar mai yawan yaɗuwa.
"Kawo yanzu an tayar da gangamin wayar da kan jama’a ga al’ummomi ta hanyar sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile yaɗuwar cutar," in ji shi.
Jami’an lafiya sun kuma ƙarfafa sa ido da matakai na mayar da martani a cikin al’ummomin da lamarin ya shafa domin gano waɗanda ake ganin sun kamu da cutar da nemo waɗanda masu cutar suka taɓa da kuma daƙile ƙarin yaɗuwar cutar.
Ɓullar cutar ta tayar da damuwa a cikin mazauna yankin, inda wasu iyalai suke ba da rahoton mutuwar ƙananan yara da ake ganin suna ɗauke da cutar.
Mashaƙo wata cuta ce da ke yawan yaɗuwa mai ƙwayoyin halitta da za ta iya haddasa wahalar numfashi mai tsanani da matsaloli na zuciya da mutuwa, musamman a cikin ƙananan yara da ba a yi wa riga kafi ba.
Nijeriya ta yi fama da ɓullar cutar mashaƙo a wasu lokuta cikin ‘yan shekarunnan, musamman a cikin ƙananan yara waɗanda ba a yi wa riga kafi yadda ya dace ba.
Cibiyar Daƙile Cututtuka masu yaɗuwa da Nijeriya (NCDC) da sauran hukumomi na tsaro sun yi kira ga iyaye da masu kula da yara su tabbatar da cewa an bai wa yara rigakafin da ake yi daga lokaci zuwa lokaci kan cutar.
Hukumar lafiya Ta Duniya ta bayyana mashaƙo a matsayin wata cuta da za a iya hanawa da riga kafi kuma ta jaddada muhimmancin gano cutar da wuri da magance ta da kuma riga kafi ga daƙile ɓullar ta.
Ɓullar cutar a jihar Filato na zuwa ne yayin da Nijeriya ke ci gaba da ƙarfafa martaninta ga cututtuka masu yaɗuwa cikin ƙalubale da suka haɗa da ƙarancin riga kafi da ƙarancin damar da jam’ian lafiya ke da ita ta shiga cikin al’ummomi da kuma jan ƙafa wajen rigakafi.
Hukumomin lafiya sun yi kira ga mazauna yankin su ba da rahoto nan-take game da duka wani da suke ganin ya kamu da cutar kuma su nema wa duk wanda suke ganin yana nuna lamun kamuwa da ta cutar mashaƙo ganin jami’an lafiya.





















