| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 262, sun kuma ceto 27 da aka yi garkuwa da su
Rundunar ’yansandan Nijeriya ta ce ta kama mutane 262 da ake zargi da aikata munanan laifuka, tare da kuɓutar da mutane 27 da aka yi garkuwa da su, a ayyukan da ta gudanar a faɗin ƙasar tsakanin ranar 5 zuwa 11 ga watan Satumba nan.
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 262, sun kuma ceto 27 da aka yi garkuwa da su
Rundunar ’yansandan Nijeriya ta kama mutane 262, ta kuɓutar da 27 da aka yi garkuwa da su a mako daya

Rundunar ’yansandan Nijeriya ta ce ta kama mutane 262 da ake zargi da aikata munanan laifuka, tare da kuɓutar da mutane 27 da aka yi garkuwa da su, a ayyukan da ta gudanar a faɗin ƙasar tsakanin ranar 5 zuwa 11 ga watan Satumba nan.

Rundunar ta kuma ce ta kwato bindigogi 34 da harsasai 375 da kuma motoci 11. An kuma kashe wasu ’yanbindiga 11 a yayin samamen.

Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa wadda CSP Aniete Iniedu ya fitar kan nasarorin da aka samu a fannin ayyukan rundunar ‘yansandan Nijeriya karkashin jagorancin Sufeto-Janar na 'Yansanda, IGP Olatunji Rilwan Disu.

Kazalika Iniedu ya ce an kama waɗanda ake zargin da laifuka da suka haɗa da garkuwa da mutane da fashi da makami da kisan kai, da kuma zarginsu da zama ’yanbindiga da ‘yan ƙungiyoyin asiri da masu safarar mutane da safarar miyagun ƙwayoyi da kuma waɗanda ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati.

Rundunar ta ce an samu rahotannin kisan kai 50 da fashi da makami 28 da garkuwa da mutane 27 da kuma hare-haren ’yanbindiga 22 a tsakanin wadannan ranakun.

A Jihar Delta, ’yansanda sun kuɓutar da wani mutum mai shekaru 60 da aka yi garkuwa da shi, bayan musayar wuta da waɗanda suka sace shi.

A jihar Sokoto, an kashe wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yanbindiga ne yayin wani samame da aka kai domin dakile wani shirin kai hari, an kwato bindigar AK-47 da harsasai 28.

A Jihar Kaduna kuwa, jami’an tsaro tare da ’yan sa-kai da mafarauta sun kai samame sansanonin ’yanbindiga, inda aka kuɓutar da mutane biyu da aka yi garkuwa da su, sannan aka kashe mutane biyu da ake zargin ’yanbindiga ne.

Sai dai ’yansanda sun ce mafarauta uku sun rasa rayukansu, yayin da wani ya samu raunin harbin bindiga.

Sai kuma Jihar Akwa Ibom, inda jami’an tsaro suka dakile wani shirin garkuwa da mutane, kana suka kwato wata bindiga da harsasai da kwale-kwale guda biyu.

Rundunar ’yansandan ta ce ana ci gaba da bincike da kuma kokarin kama sauran waɗanda ake zargi.

 

Rumbun Labarai
Majalisar Dokokin Nijeriya ta dakatar da ziyarar aiki zuwa Afirka ta Kudu
Tinubu ya bai wa kowace 'yar tawagar ƙwallon kwandon Nijeriya dala dubu ɗari-ɗari
Mutum 511 sun kamu da cutar mashaƙo a Jihar Yobe a Nijeriya
Amurka ta aika sabbin kayayyakin soji Nijeriya
Zaben Nijeriya na 2027: Matakan Tinubu na rage talauci da alƙawarin Atiku na mayar da tallafin fetur
Jakadan Nijeriya ya ziyarci ’yan kasar 198 da ke gidan yari a Indiya
Mutane da dama sun mutu yayin da wasu ke asibiti bayan sun sha wani maganin gargajiya a jihar Ondo
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta kama wasu mutane da kudade da ake zargin kuɗin fansa ne
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum biyu kan zargin kashe Danshagamu a Kano
Nijeriya ta naɗa sabon kwamandan yaƙi da ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram
NEMA ta karɓi ’yan Nijeriya 180 da aka mayar da su gida daga Libya
Sojojin Nijeriya sun kama wasu da ake zargin masu kai wa ’yanta’adda kayayyaki ne a Jihar Yobe
FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF
INEC za ta ƙaddamar da na’urar bibiyar shirye-shiryen zaɓe kai-tsaye
An  kashe mutum 12, an jikkata 2 a sabon harin da Boko Haram ta kai wani ƙauye a Adamawa ta Nijeriya
‘Yanbindiga sun kashe mutum 10, sun sace 40 a wani ƙauyen Sokoto
Gwamnatin Jihar Filato a Nijeriya ta rufe makarantu saboda ɓarkewar cutar mashaƙo
NDC ta yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa kan ba ta da ’yan takarar gwamna a jihohin Nijeriya 12
Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 36 da aka sace a kasar, sun kuma halaka ’yanta’adda da dama
‘Yanbindiga sun kashe mutum biyar tare da jikkata uku a wasu ƙauyukan Sokoto