| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF
Wasiƙar ta nuna cewa FIFA ta zartar da wannan mataki ne a taronta na ranar 1 ga Satumba a birnin Zurich, wanda ya haɗa wakilan FIFA, CAF, da NFF, da kuma gwamnatin Nijeriya.
FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF
CAF da FIFA sun dakatar da zaɓen sugbannin NFF na Nijeriya.

Makonni bayan shugabannin hukumar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya, NFF suka yi murabus, hukumar ƙwallo ta duniya, FIFA, da hukumar ƙwallo ta nahiyar Afirka, CAF sun sanar da dakatar da zaɓen NFF.

Wannan mataki ya kuma ƙunshi shirin aika tawagar hukumomin ƙwallon na duniya zuwa Nijeriya don addamar da bincike.

Tun da fari hukumar NFF ta jinkirta shirye-shiryen taron zaɓen sabbin shugabanninta da ake sa ran gudanarwa ranar 27 ga Satumban a birnin Lafia, jihar Nasarawa.

Umarnin FIFA da CAF a yanzu shi ne na dakatar da zaɓen NFF har sai tawagar haɗakar hukumomin sun isa Abuja don yin bincike kan abubuwan da suka faru a harkar ƙwallo ta Nijeriya.

Wannan na ƙunshe ne a wata wasiƙa ta ranar 7 ga Satumba, wadda babban jami’in kula da hukumomin ƙwallo mambobin FIFA, Elkhan Mammadov ya aike wa muƙaddashin mataimakin sakataren NFF, Emmanuel Ikpeme.

Wasiƙar ta nuna cewa FIFA ta zartar da wannan mataki ne a taronta na ranar 1 ga Satumba a birnin Zurich, wanda ya ƙunshi wakilan FIFA, CAF, da NFF, da kuma gwamnatin Nijeriya.

Bayan zaman taron, shugaban FIFA, Gianni Infantino ta gana da wakilan gwamnatin Nijeriya ƙarƙashin shugaban hukumar wasanni ta ƙasar, NSC, Shehu Dikko.

Takamaimen aikin tawagar zai haɗa da “duba tasirin shari’a, jagoranci, gudanarwa, da zaɓe da suka taso bayan lamuran da suka faru a NFF”.

A yanzu, shugabannin NFF na riƙo za su shirya ziyarar tawagar FIFA da CAF gabanin zuwansu Nijeriya.