| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Ministocin kasuwanci daga sassan duniya sun yi taro a ƙasar Kamaru a daidai lokacin da ake samun karuwar rikice-rikice a yankin Gabas Ta Tsakiya, lamarin da ya jefa fargaba kan hanyoyin samar da kayayyaki na duniya.
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Taron kasuwanci na Afirka / Reuters
19 awanni baya

Ministocin kasuwanci daga sassan duniya sun yi taro a ƙasar Kamaru a daidai lokacin da ake samun karuwar rikice-rikice a yankin Gabas Ta Tsakiya, lamarin da ya jefa fargaba kan hanyoyin samar da kayayyaki na duniya.

Tattaunawar da aka yi a taron ministocin Kungiyar Kasuwanci ta Duniya (WTO) a birnin Yaoundé ta zo ƙarshe ba tare da cimma wata gagarumar yarjejeniya ba da safiyar Litinin, inda mahalarta taron suka gaza dinke barakar da ke tsakanin ƙasashe kan batun sauye-sauye, aikin gona, da kuma kasuwancin intanet (e-commerce).

Bayan kwashe kwanaki hudu ana tattaunawa cikin yanayi na takaddama tsakanin Amurka, Indiya da Brazil, shugaban taron, wanda kuma shi ne Ministan Kasuwancin Kamaru, Luc Magloire Mbarga Atangana, ya bayyana cewa lokaci ya ƙure. “Mun ga cewa ba zai yiwu ba, kawai saboda dalilai na lokaci, ba wai don ba ma so ko sha’awar a cimma yarjejeniya ba,” ya shaida wa wakilan ƙasashen.

Ana kallon wannan rashin samun matsaya a matsayin koma-baya ga hadakar ciniki ta duniya. Sakataren kasuwanci na Birtaniya, Peter Kyle, ya bayyana sakamakon taron a matsayin abin takaici, yana mai cewa: “Wannan ba shi ne sakamakon da muke so ba. Birtaniya ta yi aiki tuƙuru don kawo canjin da WTO ke buƙata, kuma rashin samun matsaya ɗaya a wannan makon babban koma-baya ne ga kasuwancin duniya.”

Takaddamar Siyasar Duniya

Taron, wanda aka gudanar a matsayin taro na 14 na ministocin WTO, ya haɗa wakilai daga ƙasashe mambobi 166 a daidai lokacin da ake samun taƙaddama tsakanin ƙasashe, ciki har da rikice-rikice a yankin Gabas Ta Tsakiya waɗanda suka kawo cikas ga hanyoyin jigilar kayayyaki da makamashi.

An ɗora wa wakilan nauyin magance tabarbarewar tattalin arzikin duniya wanda ke tattare da ƙaruwar manufofin kariya da alaƙar kasuwanci.

Bayan kasuwancin intanet, ministocin sun kuma nemi ci gaba kan shawarwarin aikin gona da aka daɗe ana tattaunawa a kai, da kuma dokokin da ke kula da tallafin kamun kifi, yayin da suke kokawa da matsalolin tsarin aikin ita kanta ƙungiyar ta WTO.

Wani babban jami’in WTO da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, za a sake fara sabuwar tattaunawa.

Ministocin kasuwancin duniya sun taru ne a ƙasar Kamaru da ke tsakiyar Afirka a ranar Talata don taron ministocin WTO na 14, a daidai lokacin da rikice-rikice a Gabas Ta Tsakiya ke shafar harkokin kasuwanci.

An kafa ƙungiyar ne a shekarar 1995, kuma tana aiki ne a matsayin babban tsarin shari’a da hukumomi na kasuwancin duniya, wanda aka tsara don shiga tsakani a takaddama da kuma dakile matakan tattalin arziki.

Kokarin zamanantar da WTO ya tsananta a shekarun baya-bayan nan, musamman tun bayan taron Buenos Aires na 2017, biyo bayan kiran da aka yi na sabunta dokokin kasuwanci na intanet da zuba jari.