| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Tsohon ɗanwasan Nijeriya Eneramo ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin wasan sada zumunta
Michael Eneramo, mai shekara 40, ya faɗi a cikin fili a lokacin da ake buga wasan sada zamunta a ranar Juma'a, kamar yadda Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya ta bayyana.
Tsohon ɗanwasan Nijeriya Eneramo ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin wasan sada zumunta
Hoton da aka adana: Michael Eneramo ya buga wasanni 10 wa Najeriya. / Reuters

Tsohon ɗanwasan gaba na Nijeriya, Michael Eneramo, ya mutu bayan ya faɗi a fili yayin wasan sada zumunta ranar Juma'a.

Alamu sun nuna cewa, Eneramo mai shekaru 40, ya gamu da bugun zuciya mintuna biyar bayan dawowa daga hutun rabin lokaci a wasan sada zumuntar,' in ji Hukumar Kwallon Kafar ta Najeriya, tana ambato rahotannin farko-farko.

Eneramo ya buga wasa gaba daya kafin a tafi hutun rabin lokaci a Ungwan Yelwa da ke Kaduna, a safiyar Juma'a.

'Wannan abin tashin hankali ne matuƙa. Ba ni da kalmomin da zan iya bayyanawa a wannan lokaci,' in ji Sakatare Janar na NFF, Mohammed Sanusi.

Eneramo ya buga wa Nijeriya wasanni 10 bayan ya ƙi karɓar damar wakiltar Tunisiya, inda ya yi fice a kulob-kulob kuma yake duba yiwuwar samun shaidar zama ɗan ƙasar.

Magoya bayan ƙungiyar Espérance Sportive ta Tunis sun sanya masa suna 'The Tank', kuma, a cewar NFF, ya taimaka wa ƙungiyar wajen samun wasu kofuna. Haka kuma ya buga wasa a Turkiyya a ƙungiyoyin Sivasspor, Beşiktaş da Başakşehir, da sauran su.

Eneramo ya fara wakiltar Najeriya a wasan sada zumunta da Jamaica a Fabrairun 2009, sannan ya zura ƙwallonsa ta farko a wasan ƙasa da ƙasa a karawar da suka yi da Ireland watanni uku bayan wasan Jamaica, wanda shi ma wasa ne na sada zumunta.

Rumbun Labarai
Sojojin Nijeriya sun kashe mayakan ISWAP da dama a yankin Tafkin Chadi
Aƙalla mutum 23 ‘yanta’adda da ‘yanbindiga suka kashe a hare-hare daban-daban a arewacin Nijeriya
CBN ta gargadi 'yan Nijeriya kan yunƙurin masu kutse cikin asusun bankunan mutane
Dimokuraɗiyya za ta ɗore duk da barazanar da take fuskanta – Tinubu
An samu bullar Covid-19 a Nijeriya shekaru bayan duniya ta yi fama da ita
Tinubu ya sauke Ministan Kuɗi Edun Wale Edun da na Gidaje Ahmad Dangiwa ya ba da sunan wasu sabbi
Sojojin saman Nijeriya sun kashe tarin 'yan-ta'adda a dajin Sambisa
Nijeriya za ta gurfanar da janar mai ritaya da tsohon minista a kotu kan tuhumar su da juyin mulki
A karon farko Nijeriya ta fitar da mai fiye da wanda ta shigar cikin ƙasar
Dakarun Nijeriya sun kama masu kai wa 'yanta'adda makamai a Jihar Kogi
Dalilai uku na ɗage shari'ar tabbatar da Sarkin Kano a Kotun Ƙolin Nijeriya
NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin kwanon abinci a filin jirgin saman Legas
Farashin saniya ya kai naira N2.5m, fiye da farashin mota a Legas, in ji mahauta
Wasu na da hannu a kashe-kashe domin neman shugabanci – Ministan Tsaron Nijeriya
NBC ta yi barazanar hukunta kafafen yaɗa labaran da suke saɓa ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya
Nijeriya na neman Turkiyya ta sasanta ta da Nijar don ƙarfafa hadin kai da yaƙi da ta’addanci
An ceto masu ciki da yara da dama daga wurin da ake haifar jarirai a sayar da su a Legas
Sojojin Nijeriya sun kama mutum 14 da ake zargi da satar mai a Jihar Legas
An sace dalibai da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta jarrabawar jami’a a Nijeriya
Harin Kasuwar Jilli ba kuskure ba ne – Ministan Tsaron Nijeriya ya kare matakin rundunar soji