| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Sudan na son Turkiyya ta jawo hankalin duniya dangane da yaƙin basasar da ake yi a ƙasar
Sudan ta bayyana cewa irin dangantakar da Turkiyya ke da ita da ƙasashen Musulmi da ƙungiyar NATO ya sa take da matsayi na musamman don taimakawa wajen bayyana gaskiyar rikicin Sudan.
Sudan na son Turkiyya ta jawo hankalin duniya dangane da yaƙin basasar da ake yi a ƙasar
Amgad Fareid Eltayeb ya ce goyon bayan Turkiyya ga Sudan yana da alaƙa da dangantakar tarihi mai zurfi,

Sudan na neman Turkiyya ta taka rawar gani wajen jawo hankalin duniya kan yaƙin basasar da ake yi a cikin ƙasar, inda wani babban jami'in Sudan ya ce Ankara na da matsayi na musamman wajen wayar da kan jama'a game da rikicin da tasirinsa a yanki.

Amgad Fareid Eltayeb, mai ba shugaban Majalisar Mulki ta Sudan shawara kan harkokin siyasa da harkokin waje, ya ce goyon bayan Turkiyya ga Sudan yana da alaƙa da dangantakar tarihi mai zurfi, amma ya jaddada cewa Khartoum na fatan ganin ƙarin haɗin kai.

"Turkiyya na cikin wani matsayi na musamman don taimakawa wajen bayyana gaskiyar rikicin Sudan a kan ajandar duniya saboda dangantakarta da duniyar Musulmai da kasashen NATO," in ji Eltayeb ga Anadolu.

Yakin wanda ake yi tsakanin sojin Sudan da dakarun sa‑kai na Rapid Support Forces (RSF), ya shiga shekara ta huɗu, abin da ƙungiyoyin agaji ke cewa shi ne mafi muni ta ɓangaren buƙatun ayyukan jin ƙai a duniya.

Kira kan ayyana RSF a matsayin ƙungiyar ta'addanci

Eltayeb ya yi kira ga al'ummar duniya da su ɗauki RSF a matsayin ƙungiyar ta'addanci, yana mai cewa rikicin ba wai ƙoƙarin siyasa tsakanin shugabanni ba ne kawai, har ma ya zama wata babbar barazana ga 'yancin ƙasa da zaman lafiyar Sudan.

Ya zargi ƙungiyar da aikata laifuka marasa misaltuwa kuma ya ce wasu masu ruwa da tsaki a yankin sun goyi bayan RSF, abin da ya mayar da rikicin ya zama yaki na bayan fage tare da illoli da suka wuce iyakokin Sudan.

A cewar Eltayeb, sanya RSF a matsayin ƙungiyar ta'addanci zai iyakance hanyoyin tallafi da ke ci gaba da ɗaukar nauyin rikicin kuma zai taimaka rage rashin tsaro a yankunan Kusuwarwar Afirka, Bahar Maliya da yankin Manyan Tafkuna na Afirka da Sahel.

Gargaɗi game da rushewar ƙasa

Eltayeb ya ce kare ƙungiyoyin gwamnati na Sudan yana da muhimmanci ba wai don makomar ƙasar kaɗai ba, har ma don zaman lafiyar yanki da na Turai, yana gargaɗin cewa rushewar ƙasarsa na iya barin miliyoyin mutane a haɗarin ƙaura da rashin ƙasa.

Ya ce 'yan Sudan na so su samu tsaro, zaman lafiya da dawowar rayuwar yau da kullum, kuma ya kara da cewa canjin dimokuradiyya zai iya faruwa ne kawai idan an tabbatar da waɗannan tubalan.

Yayin da yake maraba da goyon bayan ƙasashen duniya, Eltayeb ya jaddada cewa duk wani shiri na siyasa dole ne a yi sa tare da al'ummar Sudan kuma ya nuna burinsu na makomar ƙasa.