| Hausa
NIJERIYA
4 minti karatu
ACF: Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa ta yi Allah wadai da 'cin zarafin mata' 'yan arewacin Nijeriya a Ondo
Martanin na ACF ya biyo bayan yaɗuwar wani bidiyo a kafafen sada zumunta da ke nuna jami’an Amotekun suna kamawa da kuma fito da wasu mata ’yan Arewa Hausa/Fulani a bainar jama’a, waɗanda aka ce suna zaune tare da gudanar da ayyuka a Jihar.
ACF: Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa ta yi Allah wadai da 'cin zarafin mata' 'yan arewacin Nijeriya a Ondo
ACF: Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa ta yi Allah wadai da 'cin zarafin mata' 'yan arewacin Nijeriya a Ondo / Others

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta yi kakkausar suka kan abin da ta kira baƙin fenti, kamawa da kuma barazanar korar wasu mata ’yan Arewa da jami’an Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wato Amotekun, suka yi.

A cikin wata sanarwa da Shugaban Kwamitin Amintattu na ƙungiyar, Bashir M. Dalhatu, ya fitar, ƙungiyar ta bayyana waɗannan matakai a matsayin na wariya waɗanda suka saɓa wa kundin tsarin mulki da kuma take haƙƙoƙin da doka ta ba dukkan ’yan Nijeriya.

Martanin na ACF ya biyo bayan yaɗuwar wani bidiyo a kafafen sada zumunta da ke nuna jami’an Amotekun suna kamawa da kuma fito da wasu mata ’yan Arewa Hausa/Fulani a bainar jama’a, waɗanda aka ce suna zaune tare da gudanar da halastattun ayyuka a Jihar Ondo.

A cewar ACF, duk wani yunƙuri na tsoratarwa ko korar ’yan Nijeriya saboda asalinsu na ƙabila ko yanki na tauye ginshiƙan da aka kafa ƙasar a kansu.

“Yunƙurin da jami’an Amotekun na jihar Ondo suka yi na tantancewa, tsoratarwa da kuma yi wa ’yan Nijeriya barazanar mayar da su jihohinsu ko yankunansu na asali abu ne mai matuƙar tayar da hankali,” in ji ƙungiyar.

ACF ta jaddada cewa kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba kowane ɗan ƙasa damar zirga-zirga cikin ’yanci, zama da gudanar da halastattun ayyukan tattalin arziki a ko’ina cikin ƙasar ba tare da nuna masa wariya saboda ƙabila, addini, harshe ko wurin haihuwa ba.

Ƙungiyar ta kuma lura cewa babu wata gwamnatin jiha, rundunar tsaro ko hukuma ta ƙaramar hukuma da ke da ikon doka na korar ’yan Nijeriya daga wani yanki na ƙasar zuwa wani.

 “Babu wani tanadi a dokokin Nijeriya da ke bai wa wata gwamnati ta jiha ko rundunar tsaro ko hukuma ta ƙaramar hukuma ikon korar ’yan Nijeriya daga wani ɓangare na tarayya zuwa wani. Kowane ɗan Nijeriya yana da cikakken hakki a kowane yanki na ƙasar,” in ji sanarwar.

ACF ta nuna damuwa musamman ganin cewa waɗanda abin ya shafa mata ne da ke gudanar da halastattun ayyukan tattalin arziki, tana mai bayyana abin da ake zargin an yi musu na wulakanci a bainar jama’a a matsayin abin da ba za a amince da shi ba a cikin tsarin dimokuraɗiyya.

Duk da amincewa da ƙalubalen tsaro da ke addabar sassa da dama na ƙasar, ACF ta ce ya kamata yaƙi da laifuka ya dogara ne kan sahihan bincike, tattara bayanan sirri da aiwatar da doka bisa hujjoji, ba wai ware mutane bisa ƙabila ba.

“Ba za a iya ɗora wa al’umma baki ɗaya laifi saboda ayyukan wasu tsirarun mutane ba. Yin hakan zalunci ne, ba shi da amfani kuma yana iya haifar da rikicin ƙabilanci,” in ji ƙungiyar.

Ta yi gargaɗin cewa irin waɗannan matakai na iya yin barazana ga haɗin kan ƙasa da zaman lafiya, tana mai nuni da cewa dubban mutane daga jihar Ondo da sauran jihohin Kudu maso Yamma suna rayuwa, aiki da gudanar da kasuwanci a Arewacin Nijeriya ba tare da fuskantar tsangwama ba.

ACF ta yi kira ga gwamnatin Jihar Ondo da ta binciki lamarin, ta fayyace yadda ya faru tare da ɗaukar matakin da ya dace kan duk wani jami’i da aka samu ya karya doka.

Haka kuma, ƙungiyar ta buƙaci Gwamnatin Tarayya, hukumomin tsaro da Hukumar Kare Hakkin Bil’adama da su binciki lamarin tare da tabbatar da kare haƙƙin tsarin mulkin waɗanda abin ya shafa.

Bayan wannan lamari, ACF ta ce abin da ya faru ya sake tayar da damuwa kan muhawarar da ake yi game da ’yan sandan jihohi, tare da nuna buƙatar samar da kariya mai ƙarfi ta kundin tsarin mulki da cibiyoyi domin hana cin zarafi, wariya da amfani da ikon tsaro ba daidai ba.

“Nijeriya ta kowane ɗan Nijeriya ce. Bai kamata a taɓa ɗaukar wani ɗan ƙasa a matsayin baƙo a cikin ƙasarsa ba,” in ji sanarwar.