| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Shugaban Nijeriya ya nuna goyon baya ga kasashen Gulf game da yaƙin Iran
Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ya jinjina wa ƙasashen yankin Gulf kan juriyarsu da kai zuciya nesa yayin yaƙin Iran.
Shugaban Nijeriya ya nuna goyon baya ga kasashen Gulf game da yaƙin Iran
Jakadan Saudi Arabia, Yousef Bin Mohammed Albalawi, ya gabatar da takardar amincewarsa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Fadar Gwamnati, Abuja. / Others

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana goyon baya ga ƙasashen yankin Gulf a yayin da yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi kan Iran ke gudana.

Shugaban ya yaba wa ƙasashen saboda juriya da kauce wa tashin hankali yayin wannan yaƙi.

“Nijeriya na bayyana cikakken goyon baya ga Saudiyya, Qatar, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, Kuwait, Bahrain, Oman, da Jordan, a yanayin hare-haren baya-bayan nan, kuma muna cewa za mu ci gaba da ƙoƙarin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin duniya,” in ji shugaban a ranar Alhamis a cewar wata sanarwa daga kakakinsa.

Sanarwar ta ƙara ce, “Duniya na buƙatar natsuwa, zaman lafiya da ƙauna. Muna nuna wannan goyon baya ga dukkanku a yankin”.

Shugaba Tinubu ya furta wannan a Fadar Shugaban a Abuja, lokacin da ya karɓi wasiƙun shaida daga jakadu bakwai da manyan kwamishinonin diflomasiyya biyu, ciki har da na Qatar da Saudiyya.

Amurka da Isra'ila sun ƙaddamar da hare-hare tare kan Iran ranar 28 ga Fabrairu, abin da ya sa Iran ta mayar da martani da hare-hare kan Isra'ila da wasu ƙasashen da ke masaukin kadarorin sojin Amurka a yankin.

Shugaba Donald Trump ya tsawaita tsagaita wuta da Iran domin bai wa tattaunawar neman yarjejeniya ƙarin lokaci, amma ya ce Amurka za ta ci gaba da rufe tashoshin ruwa na Iran.

Tsawaita tsagaita wutar da Trump ya yi ta zo cikin 'yan awanni kafin a tsohuwar tsagaita wutar ta ƙare.