| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Aƙalla mutum 23 ‘yanta’adda da ‘yanbindiga suka kashe a hare-hare daban-daban a arewacin Nijeriya
Aƙalla mutane 23, ciki har da yara kanana uku ‘yanta’adda da ‘yanbindiga suka kashe a ranar Talata a hare-hare daban-daban a arewa maso-gabas da arewa maso-yammacin Nijeriya, in ji rahotannin jami’an tsaro.
Aƙalla mutum 23 ‘yanta’adda da ‘yanbindiga suka kashe a hare-hare daban-daban a arewacin Nijeriya
A report to the UN shows that suspected Boko Haram terrorists and bandits recently killed at least 23 people in separate attacks in northern Nigeria. / AA

Aƙalla mutane 23, ciki har da yara uku, aka kashe a ranar Talata sakamakon hare-hare uku daban-daban da aka ɗora alhakinsu kan 'ya ta'adda da ƙungiyoyin masu aikata laifuka a arewa maso gabashi da arewa maso yammacin Nijeriya, a cewar wani rahoto.

Wasu 'yanta'adda da ake zargin 'yan Boko Haram ne sun kashe mutum 11 a wani hari da suka kai a wani ƙauye a arewa maso gabashin jihar Borno, yayin da wasu 12 suka mutu a hare-haren da aka kai a ƙauyuka biyu a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Nijeriya, a cewar rahotanni guda biyu da jami’an tsaro suka fitar.

Wasu 'yanta'adda da ake zargin 'yan Boko Haram ne a kan babura da dama sun kai hari a al'ummar Pubago da ke gundumar Rumirgo a Borno a daren ranar Talata, a cewar ɗaya daga cikin rahotannin.

Rahoton ya ce har yanzu ba a ga wasu mazauna yankin ba, yana mai gargadin cewa adadin zai iya karuwa.

Hare-Hare daban-daban

A wasu hare-hare daban-daban a rana guda, 'yan bindiga sun kai hari a kauyukan Rumbuki da Nikai a gundumar Bukkuyum ta jihar Zamfara, in ji wani rahoton.

Maharan da ke kan babura da dama, sun kai hari a Rumbuki, "sun kashe mutane tara tare da raunata wasu mazauna takwas", inda wasu mutanen da dama suka bace, rahoton ya bayyana.

Sun kashe akalla "yara uku" a harin da aka kai a kauyen Nikai.

Ƙaruwar haɗin gwiwar 'yan bindiga da 'yan ta'adda ya zama abin damuwa ga hukumomi da masu sharhi.

Sojoji sun ce sun himmatu wajen kakkaɓe 'yan ta'adda da 'yan fashi a yankunan.

A cikin 'yan kwanakin nan 'yanta'addar Boko Haram, sun tsananta kai hare-hare kan sansanonin soji da al'ummomi a arewa maso gabas, wanda ya haifar da asarar fararen-hula da sojoji ciki har da manyan kwamandojin soji.

'Yanbindiga sun ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, suna kashe mazauna, sace mutane don neman fansa da kuma wawushe kayan da ke cikin gidaje kafin su ƙona su.

Sojojin Nijeriya sun ce har yanzu suna jajircewa wajen kakkaɓe 'yanta'adda da 'yanfashi a kasar.


Rumbun Labarai
Sojojin saman Nijeriya sun kashe tarin 'yan-ta'adda a dajin Sambisa
Nijeriya za ta gurfanar da janar mai ritaya da tsohon minista a kotu kan tuhumar su da juyin mulki
A karon farko Nijeriya ta fitar da mai fiye da wanda ta shigar cikin ƙasar
Dakarun Nijeriya sun kama masu kai wa 'yanta'adda makamai a Jihar Kogi
Dalilai uku na ɗage shari'ar tabbatar da Sarkin Kano a Kotun Ƙolin Nijeriya
NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin kwanon abinci a filin jirgin saman Legas
Farashin saniya ya kai naira N2.5m, fiye da farashin mota a Legas, in ji mahauta
Wasu na da hannu a kashe-kashe domin neman shugabanci – Ministan Tsaron Nijeriya
NBC ta yi barazanar hukunta kafafen yaɗa labaran da suke saɓa ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya
Nijeriya na neman Turkiyya ta sasanta ta da Nijar don ƙarfafa hadin kai da yaƙi da ta’addanci
An ceto masu ciki da yara da dama daga wurin da ake haifar jarirai a sayar da su a Legas
Sojojin Nijeriya sun kama mutum 14 da ake zargi da satar mai a Jihar Legas
An sace dalibai da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta jarrabawar jami’a a Nijeriya
Harin Kasuwar Jilli ba kuskure ba ne – Ministan Tsaron Nijeriya ya kare matakin rundunar soji
Shuguba Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin kudin Nijeriya na 2026, ya tsawaita wa'adin na 2025
Abin da ya sa Kungiyar Tuntuba ta Arewa ta ce Nijeriya ta shiga yanayi na yaƙi
Nijeriya ta yi gargaɗi kan 'shirin kai harin ta'addanci' kan kayayyakin more rayuwa a Abuja da Neja
Kamfanonin jiragen saman Nijeriya sun yi barazanar dakatar da aiki saboda tashin farashin man jirgi
NACA ta yi gargadi game da yaɗa bayanan HIV ba bisa ƙa'ida ba a shafukan sada zumunta a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta ce jihohi 33 da al'ummomi 14,000 na cikin hadarin ambaliyar ruwa a 2026