Idan Afirka tana neman hujjar cewa kawar da cututtukan yankuna masu zafi da aka yi watsi da su (NTDs) ba wai kawai zai yiwu ba ne, abu ne da za a iya cim mawa tsawon lokuta, ba sai ta yi duba ga nesa ba kawai ta kalli Togo, ƙasar da ke a cikin nahiyar.
A yankin da aka daɗe ana aminta da cututtukan NTDs a matsayin cututtuka da ke da alaƙa da talauci, Togo ta zaɓi ta wargaza wannan lamari- kuma ta yi nasara.
Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana Cututtukan da aka yi watsi da su a yankuna masu zafi (NTD) a matsayin rukuni na cututtuka 21 waɗanda "ke shafar talakawa da marasa galihu" kuma suna bunƙasa a cikin yanayin talauci, rashin tsafta, da ƙarancin damar samun kiwon lafiya.
An bayyana su a matsayin "wadanda aka yi watsi da su" saboda a tarihi ba su sami kulawa da kuɗaɗen da suka dace ba idan aka kwatanta da sauran manyan cututtuka, duk da cewa sun shafi kusan mutane biliyan 1.5 a duk duniya.
Togo ta ja ragamar
A shekarar 2022, ƙasar Yammacin Afirka ta zama ƙasa ta farko a Afirka kuma daga cikin huɗu kacal a duniya da suka kawar da cututtukan yankuna masu zafi guda huɗu da aka yi watsi da su a matsayin barazanar lafiyar jama'a: Dracunculiasis (cutar tsutsotsi ta Guinea), lymphatic filariasis, trypanosomiasis ta Afirka ta ɗan adam (cutar barci) da trachoma.
Amma abin da ya sa Togo ta zama abin mamaki ba wai kawai ta kawar da cututtukan ba ne. Ko da bayan ta kai wani matsayi da ƙasashe da yawa ke bi har yanzu, ba ta dakata ba. Madadin haka, ta sanya ido kan kawar da ƙarin cututtuka nan da shekarar 2030, da suka hada da ciwon daji, tsargiya, kuturta da cutar lagwada.
A watan Janairun wannan shekarar, Togo ta sanar da cewa za ta yi watsi da rashin gamsuwar da ke biyo bayan nasara kuma za ta "nuna jagoranci" a yaƙi da cututtuka.
Ma'aikatar Lafiya ta Togo, a cikin wata sanarwa, ta bayyana kudurin "kawar da cututtuka kamar su ciwon daji, tsargiya, kuturta da lagwada, tana mai jaddada cewa wadannan cututtukan suna da "tasiri mai ɗorewa kan inganci da yawan ayyuka, makaranta da kudin shiga na gida, musamman a yankunan karkara."
Dr. Mamadou Nouhou, wakilin Hukumar Lafiya ta Duniya a Togo, a lokacin bikin Ranar NTD ta Duniya a wannan shekarar, ya ce kasar ta Yammacin Afirka ta kuduri aniyar "ba za ta bar kowa a baya ba."
Dr. Elizabeth Juma, Shugabar Tawagar Fadadden Aikin Musamman don Kawar da NTDs (ESPEN) - wani shiri na hadin gwiwa da WHO ke jagoranta - ta nuna cewa labarin nasarar Togo yana bai wa nahiyar wani abu mai mahimmanci fiye da zaburarwa - tabbataccen tsari.
"Ba wai kawai a baki ba ne... A aikace ne, amma batu ne na shugabanci. Togo ta yi aiki tare da abokan hulɗa na duniya - amma bisa ga sharuddanta. Gwamnati ta tsara dabarun aiki, tana nanata cewa wannan shi ne abin da muke son yi," Juma ta shaida wa TRT Afrika.
Cigaban da ba a saba gani ba
Tun daga farkon shekarar 2026, ƙasashen Afirka 22 sun kawar da aƙalla cututtukan da aka yi watsi da su a yankuna masu zafi. Masana sun ce Afirka ba ta gaza a yaƙinta da NTDs ba; a fannoni da yawa, tana ƙara ƙarfi.
"Abin takaici, ba ma kan manufar cim ma burin (MDD) da aka tsara na 2030 ba," in ji Dr Juma.
Wannan gibin ba ya faru ne saboda rashin ilimi ko ma jajircewa ba. Ya samo asali ne daga raunin tsarin da ya daɗe yana kula da lafiyar jama'a a yawancin nahiyar. Babban cikinsu shi ne dogaro - musamman kan kuɗaɗen kasashen waje.
Raguwa a hankali na tallafin cigaba daga ƙasashen waje bayan annobar COVID-19 ya bayyana yadda shirye-shiryen ƙasa da yawa suka zama masu hatsari. Lokacin da manyan masu ba da gudunmawa suka rage tallafi, shiga tsakani ya ragu, lokaci ya yi karanci, kuma a wasu lokutan, shirye-shiryen na fuskantar hatsarin tsayawa.gaba ɗaya.
"Idan kuɗi ya ragu sosai, to yana nufin mun yi watsi da komai," in ji Dr Juma. "Muna fuskantar hatsarin rasa duk wannan babban jarin da aka zuba."
Masana sun ce hatsarin shi ne Cututtukan da aka yi watsi da su a yankuna masu zafi ba su da afuwa domin idan aka katse gangamin yin magani ko sa ido, za su dawo - kuma za su iya yaɗuwa da sauri fiye da yadda aka kore su. Shekaru na cigaba na iya wargajewa da sauri, suna mayar da al'ummomi cikin yanayin nakasa, ƙyama da talauci.
Wannan shi ne inda misalin Togo ya zama mafi aki da ilimi fiye da zama na musamman.
Nasararta ba ta ginu bisa ga kuɗaɗen da ba a saba gani ba ko yanayi mai kyau. An gina ta ne bisa zaɓi. Jagorancin siyasa wanda ya wuce magana da baki kawai kuma ya saka kawar da NTD cikin manufofin ƙasa.
Jami'an gwamnati sun tsara burin ta hanyar faɗaɗawa, suna jaddada cewa kawar da waɗannan cututtuka ba wai kawai batun lafiya ba ne, muhimmin mataki ne na karya halin talauci da cim ma "daidaito a fannin lafiya."
"Dabarar ta dogara ne akan faɗaɗa gangamin yin riga-kafi da bayar da magani kyauta. Haka kuma yana da nufin ƙarfafa shirye-shiryen wayar da kan jama'a, horar da ma'aikatan lafiya, da inganta damar samun ayyukan kiwon lafiya a yankunan karkara da na nesa," in ji wata sanarwa da gwamnati ta fitar a watan Janairu.
Darasi ga nahiyar
Wannan yanayi na mallakar ƙasa—wanda ke kawo fifiko, tattara albarkatu da kuma dagewa kan ci gaba—na iya zama darasi mafi muhimmanci da Togo ke bayarwa.
A tsawon lokaci, shirye-shiryen kiwon lafiya da yawa na Afirka an tsara su a kasashen waje, suna barin su cikin rauni lokacin da fifiko ya sauya ko kuma kuɗi ya ragu. Togo ta juya wannan dangantakar. Ta fara bayyana manufofinta kuma ta gayyaci abokan hulɗa su hada kai da su.
“Togo ba ta bar abokan hulɗa su tsara abin da za a yi ba. Gwamnati ce ta tsara dabarun kuma ta ce, 'Wannan shi ne abin da muke son yi.' 'Ga inda muke son zuwa.' 'Wannan shi ne abin da muke yi.' 'Me za ku iya kawo wa don taimaka mana mu cim ma wannan burin?' Sun yi aiki mai kyau a jagoranci," in ji Juma.
Masana sun kuma yi kira ga cibiyoyin bincike na gida da su karfafa ayyukanmu na ganin ko jami'o'i ne ko cibiyoyin bincike na lafiya masu zaman kansu ne za su gudanar da bincike.
"Rage kudaden da gwamnatoci ke kashewa a duniya ya riga ya yi tasiri sosai kan bincike," in ji Mataimakin Darakta, Farfesa Nicki Tiffin, da ke Cibiyar Nazarin Halittu ta Ƙasa ta Afirka ta Kudu yayin tattaunawa da TRT Afrika. "Ilimin cibiyoyi ne ke ɓacewa. Rashin ilimi mai zurfi. Muna rasa mutane masu ƙwarewa daga wurin ƙirƙirar hanyoyin kiwon lafiya."
Farfesa Iruka Okeke, masaniyar ƙwayoyin cuta ta Najeriya, ta maimaita waɗannan damuwar, tana hakaito hulɗarta da masu bincike masu tasowa a faɗin Najeriya.
"A Najeriya, masana da binciken kimiyya na rasa hazaka a wani yanayi mai ban tsoro. Matasan masana kimiyya da muke ɗauka suna bayyana mana a fili cewa suna da niyyar barin aiki ko da a farkon samun horonsu saboda ba za su iya tunanin aikin kimiyya mai amfani a nan ba", Okeke ta shaida wa TRT Afrika.
Labari mai daɗi shi ne cewa ƙasashen Afirka da dama sun fara saba wa tare da koyo, a cewar Juma.
"Ma'aikatun lafiya na ƙasashen Afirka da yawa sun ce, za mu sami tsarin shirye-shirye iri ɗaya. A ƙarshe, ba za mu sami cikas ba fiye da yadda ake tsammani."
A wurare kamar Tanzania, Uganda da Madagascar, tsarin kiwon lafiya ya sake tsara kansa, yana haɗa shirye-shirye, yana raba albarkatu da kuma fifita aiki mai inganci.
Juma ta yi imanin cewa a nan ne ainihin jarrabar Afirka take. Ba wai ko za ta iya kwaikwayon dabarun fasaha na Togo ba, a’a sai dai batun ko za ta iya dabbaka tunaninta: ƙin karɓar alhakin da kuma jajircewa ga ci gaba.















