| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Dakarun Nijeriya sun kai samame a sansanin 'yanta'addan IPOB
Dakarun Nijeriya sun kama wasu daga cikin masu aikata laifuka tare da ƙwace makamai da kuɗaɗe daga gare su.
Dakarun Nijeriya sun kai samame a sansanin 'yanta'addan IPOB
Tsohon hoto: Dakarun Nijeriya suna yaƙar masu tayar da ƙayar baya a sassan ƙasar / Reuters

Dakarun sojin Nijeriya sun zafafa kai samame a sansanin 'yanta'addan IPOB’ESN a faɗin kudu maso gabashin ƙasar inda suka lalata maɓoyar tare da ƙwace makamai.

Wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar a shafinta na X ranar 15 ga watan Afrilu ta ce wani samame da dakarun runduna ta musamman ta Operation Eastern Sanity suka kai dajin Ajali, a ƙaramar hukumar Ezeagu ta jihar Enugu ranar 14 ga watan Afrilu ya tilasta wa ‘yanta’addan IPOB/ESN tserewa inda suka bar kayayyakinsu ciki har da nakiyar tarwatsa tankokin yaƙi.

“Tawagar jami’an tsaro ta kawar da abubuwa masu fashewa da ta samu a wurin, inda ta hana yiwuwar yin lahani ga dakaru da fararen-hula,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa dakarun sun lalata sansanonin da mayaƙan ke ɓuya ta yadda ba za su iya sake haɗuwa a wuraren ko kuma su samu wata kariya a wuraren ba.

A wani samame makamancin hakan a ranar Talatan, dakarun da aka tura Adani a ƙaramar hukumar Uzo-Uwani, da suke aiki bisa bayanan sirrin da suka samu daga jami’an tsaro na farin kaya DSS, sun bi sawu tare da kama wani kuɗin fansa da ke da alaƙa da wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane.

Masu AlakaTRT Afrika - 'Yansanda a Nijeriya sun kama mutum 33 kan zargin satar mutane a coci

“Samamen ya sa an kama wani ƙasurgumin wanda ake zargi da garkuwa da mutane, lamarin da ya sake bayyana yadda ƙungiyar ke dogaro kan aikata laifuka wajen ɗaukar nauyin gudanar da ita,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa bincike a wurin ya sa an samu wata bindiga da kuma kuɗi da ya kai naira miliyan biyu (₦2,000,000), wanda aka yi imanin cewa kuɗin fansa ne daga gidan wanda ake zargin.

“Wanda ake zargin da abubuwan da aka ƙwacen an miƙa su ne ga hukumomin da suka dace domin cikakken bincike domin gano sauran ‘yan ƙungiyar masu aikata laifukan,” in ji sojin.

Ta ƙara da cewa wannan aikin ya ƙara kassara ikon IPOB/ESN na aika-aika ko na kudi, wanda ya nuna cewa ƙungiyar tana rasa tagomashi a ƙarƙashin matsi na soji, in ji sanarwar.

Ta jaddada cewa sojin za ta ci gaba da matsa wa masu aikata laifuka da kuma hana su wuraren ɓuya a fadin yankin.

Rumbun Labarai
Wasu na da hannu a kashe-kashe domin neman shugabanci – Ministan Tsaron Nijeriya
NBC ta yi barazanar hukunta kafafen yaɗa labaran da suke saɓa ƙa’idojin aikin jarida a Nijeriya
Nijeriya na neman Turkiyya ta sasanta ta da Nijar don ƙarfafa hadin kai da yaƙi da ta’addanci
An ceto masu ciki da yara da dama daga wurin da ake haifar jarirai a sayar da su a Legas
Sojojin Nijeriya sun kama mutum 14 da ake zargi da satar mai a Jihar Legas
An sace dalibai da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta jarrabawar jami’a a Nijeriya
Harin Kasuwar Jilli ba kuskure ba ne – Ministan Tsaron Nijeriya ya kare matakin rundunar soji
Shuguba Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin kudin Nijeriya na 2026, ya tsawaita wa'adin na 2025
Abin da ya sa Kungiyar Tuntuba ta Arewa ta ce Nijeriya ta shiga yanayi na yaƙi
Nijeriya ta yi gargaɗi kan 'shirin kai harin ta'addanci' kan kayayyakin more rayuwa a Abuja da Neja
Kamfanonin jiragen saman Nijeriya sun yi barazanar dakatar da aiki saboda tashin farashin man jirgi
NACA ta yi gargadi game da yaɗa bayanan HIV ba bisa ƙa'ida ba a shafukan sada zumunta a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta ce jihohi 33 da al'ummomi 14,000 na cikin hadarin ambaliyar ruwa a 2026
'Yansanda a Nijeriya sun kama mutum 33 kan zargin satar mutane a coci
Turkiyya ta raba tallafin tan 36 na abinci ga 'yan gudun hijira a Nijeriya
Tana ƙasa tana dabo game da yiwuwar babban taron Jam'iyyar ADC a Nijeriya
'Yanta'adda sun kai hari sansanin sojin Nijeriya, sun kashe kwamanda da sojoji shida
Nijeriya na neman tallafin IMF da Bankin Duniya don rage tasirin yakin Iran kan tattalin arziki
Me ya sa hare-hare ke karu wa a Nijeriya duk da wanzuwar dakarun Amurka?
Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta soma bincike kan zargin kisan fararen-hula a kasuwar Jilli ta Yobe