Trump ya sa tawagogin kasashen Afirka cikin matsala a gasar Kofin Duniya na FIFA 2026
Shugaban Amurka Donald Trump yana riƙe da Kofin Duniya na FIFA a cikin Ofishin Oval a Fadar White House. / Reuters
Trump ya sa tawagogin kasashen Afirka cikin matsala a gasar Kofin Duniya na FIFA 2026
An shirya fara gasar a watan Yuni, kuma ana sa ran ta zama mai tarihi saboda nahiyar Afirka ta samu mafi girman adadin wakilci, amma a yanzu halartar ƙasashen Afirka ta zama mai cike da matsala.

Tawagogin ƙwallon ƙafa na ƙasashen Afirka suna cikin mawuyacin hali yayin da babbar gasar ƙwallon ƙafa ta duniya, Kofin Duniya na FIFA ke ƙaratowa.

Kungiyoyi arba'in da takwas da kuma ƙasashe uku masu masaukin baƙi, wato Amurka, Mexico, da Canada suna shirin tunkarar gasar.

Ga Afirka, wannan gasar, wadda za a fara a watan Yuni, ya kamata ta kasance mai cike da tarihi, saboda nahiyar Afirka ta samu mafi girman adadin wakilci. Amma alamu na nuna akwai matsala. Kuma ga dililin

Senegal da Ivory Coast na cikin jerin ƙasashen da dokar hana tafiya ta Donald Trump ta shafa. Wannan dokar ba wai Afirka kaɗai ta shafa ba. Haka ma ta shafi Haiti, wata ƙasa ta yankin Caribbean da magoya bayanta za su iya fuskantar irin waɗannan takunkumai.

Wannan babbar matsala ce. An tsara waɗannan ƙungiyoyi su buga wasannin rukuni a Amurka. Senegal za ta fafata da Faransa a New York, yayin da Ivory Coast za ta buga da Ecuador a Philadelphia.

Magoya baya na iya kasa shiga

‘Yan wasan za su kasance a wurin, amma yawancin magoya bayansu za su iya rasa damar shiga Amurka.

Takunkumin hana biza ba shi ne kaɗai ƙalubale ba. Ta’azzarar rikici a yankin ya ƙara wani sabon mataki na rashin tabbas.

A ranar 28 ga Fabrairu, Amurka da Isra'ila sun ƙaddamar da hare-hare kan Iran. Nan take Qatar ta ɗage dukkan harkokin wasannin a watan Maris, ciki har da wasannin shiri tare da Masar da wasu ƙasashen Afirka da suka dogara da waɗannan shirye-shiryen.

Rufe sararin samaniya a wasu sassan Gabas ta Tsakiya yanzu yana kawo cikas ga hanyoyin tafiya da ƙungiyoyin Afirka da yawa ke amfani da su wajen zirga-zirga tsakanin Turai da nahiyar Arewacin Amurka.

Halin da Masar ke ciki ya fi rikitarwa. An sa su a rukuni ɗaya da Iran, ƙasar da yanzu ke cikin rikici kai-tsaye da ɗaya daga cikin ƙasashen da ke ɗaukar baƙuncin gasar, wato Amurka.

Idan wannan yanayin ya rincaɓe, Masar na iya samun kanta cikin rukunin da wasannin ba lallai su faru ba.

An matsar zuwa gefen

Wannan ba zai zama karo na farko ba da Afirka ta samu kanta a gefe guda a gasar kofin duniya.

A shekarar 1966, dukan ƙasashen Afirka sun janye daga jerin neman cancanta gasar don nuna adawa bayan FIFA ta ba Afirka, Asiya, da Oceania gurbi guda ɗaya na haɗin-gwiwa a gasar da aka yi a Ingila.

Shi ne kaɗai karon da aka buga gasar Kofin Duniya a tarih, inda nahiyar bakiɗaya ta yi ƙaurace wa gasar.

Afirka ta yi fafutukar neman wakilci. Kuma a yau tana da ƙungiyoyi tara, wato Senegal, Maroko, Tunisiya, Guinea, Aljeriya, Ghana, Cape Verde, Masar da Afirka ta Kudu.

Amma fa samun wakilci ba tare da damar halartar iyalai da magoya baya ba zai zama abin nuni kawai.

Rumbun Labarai
Iran ta ce dole Amurka ta ba da biza ga tawagarta ta Kofin Duniya ba tare da la'akari da siyasa ba
Karawar PSG da Bayern Munich za ta sake kayatarwa
Kungiyoyin Gasar Firimiya ta Ingila sun yi asarar dala biliyan 1 na kudin-shiga: Rahoto
Neymar ya yi dambe da ɗan Robinho a haduwarsu ta farko a filin atisaye na Santos
CAF ta tabbatar da ranakun gasar AFCON 2027 a Kenya, Tanzania da Uganda
Iran za ta buga wasannin Gasar Kwallon Kafa ta Duniya a Amurka duk da rikici, in ji FIFA
Tsohon ɗanwasan Nijeriya Eneramo ya mutu sakamakon bugun zuciya yayin wasan sada zumunta
Iran 'ba ta ƙarƙare yanke hukunci' kan halartar Kofin Duniya na 2026 a Amurka ba
Tottenham na neman masanin lafiyar tunani ga ‘yanwasanta, don gujewa fadowa daga gasar Firimiya
'Na yi imanin Arsenal ce za ta ɗaga Kofin Firimiya' - Arsene Wenger
Guardiola ya ce zai sallama Kofin Firimiya idan Man City ta sha kashi a hannun Arsenal
Nijeriya ta yi maraba da 'yarwasan tsere, Favour Ofili wadda aka hana ta sauya kasar da take wakilta
Shugaban FIFA ya ce akwai ‘tabbacin’ Iran za ta halarci Gasar Cin Kofin Duniya
Hukumar FA ta ci tarar Harry Maguire saboda rashin ɗa'a a wasan Man United da Bournemouth
UEFA ta yi watsi da korafin Barcelona kan wasan da Atletico Madrid ta doke su
Masoyin Arsenal ɗan Uganda na barazanar kai Gunners kotu kan damuwar da ya shiga bayan shan kaye
Danwasan Ghana, Kudus ya samu rauni a Tottenham, zai iya gaza zuwa gasar Kofin Duniya ta 2026
Anthony Joshua 'zai koma damben boksin' bayan mummunan hatsarin mota
Mbappe da Vinicius za su koma aiki tare a wasan Real Madrid da Bayern Munich
Ghana ta kori kocinta Addo makonni gabanin gasar cin kofin duniya