Erdogan ya mika godiyarsa ga tsoffin sojojin da suka yi yakin na samar da zaman lafiyar. / Hoto: AA

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya isa Arewacin Cyprus ta Jamhuriyar Turkiyya domin halartar bukukuwan cika shekaru 50 da fara aikin samar da zaman lafiya a Cyprus da aka fi sani da ranar zaman lafiya da 'yanci.

"Turkiyya a shirye take don tattaunawa da samar da zaman lafiya mai dorewa da mafita a Cyprus", in ji shugaba Erdogan a ranar Asabar.

Yin watsi da hakikanin abin da ke faruwa a tsibirin Cyprus ba zai kai ko'ina ba, kamar yadda shugaban kasar Turkiyya Erdogan bayyana.

Erdogan ya jaddada goyon bayan Turkiyya ga TRNC, yana mai cewa, "Muna ci gaba da goyon bayan TRNC, wadda aka kafa da jinin shahidanmu, domin ta zama kasa mai karfi, wadata, da mutuntawa."

Ya kuma bayyana fatansa dangane da nan gaba, yana mai cewa: "Ina fatan za mu ga ranar da shugabannin kasashen da suka amince da tsibirin za su ziyarci duka ƙasashen a tare."

Tunawa da sojojin Turkiyya

Shugaban kasar Cyprus Ersin Tatar ya tarbi Erdogan a filin jirgin sama na Ercan da ke Lefkosa babban birnin kasar. Bayan bikin maraba, Erdogan ya ajiye fure a gidan tarihi na Ataturk da ke birnin tare da sanya hannu kan littafin na musamman na wurin.

“Muna jin daɗin cika shekaru 50 da fara aikin samar da zaman lafiya a ranar 20 ga watan Yuli, wanda jaruman sojojin mu suka yi kafada da kafada tare da al’ummar Cyprus ta Turkiyya.

"Al'ummar Turkiyya sun sake nuna wa duniya irin jajircewar da suke yi na samun 'yancin kai da kuma makomarsu ta wannan aiki. Al'ummar Cyprus ta Turkiyya na ci gaba da fafutukar neman 'yancin kai, tare da samun nasara tare da goyon bayan uwar kasar Turkiyya, kuma suna sa ido kan makomarsu tare fata da kwarin gwiwa," kamar yadda Erdogan ya rubuta a littafin.

Ya kuma tuna da sojojin Turkiyya da suka “bar wannan kasar a matsayin kasarsu ta haihuwa,” sannan ya mika godiyarsa ga tsoffin sojojin da suka yi yakin samar da zaman lafiyar.

AA