Yara su ne kashi 40 cikin 100 na mutanen da ke gudun hijira a duniya, a cewar Majalisar Dinkin Duniya. / Hoto: AFP

Rikice-rikice da ake fama da su a ƙasashen Mali da Burkina Faso da Nijar, sun tilasta wa yara kusan miliyan 1.8 barin gidajensu, wanda ke nuna ƙaruwar hakan sau biyar cikin shekaru biyar da suka gabata, in ji ƙungiyar agaji ta Save the Children a ranar Alhamis.

Ƙungiyar mai zaman kanta ta ƙididdige adadin yaran da suka rasa matsugunansu a ƙasashen Sahel uku ta hanyar yin nazari kan aƙaluman hukumar kula da ƴan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) da gwamnatocin ƙasashe da kuma ƙungiyar kula da masu ƙaura ta duniya (IOM).

Binciken ya nuna cewa adadin yaran da aka tilasta wa barin gidajensu ya ƙaru daga kusan 321,000 a shekarar 2019 zuwa kusan miliyan 1.8 a yanzu.

"Rikicin, wanda aka manta da shi a tsakiyar Sahel ya kasance ɗaya daga cikin mafi munin bala'in gaggawa na jinƙai a duniya, wanda ya fi muni la'akari da yadda cewa wannan rikicin ya fi shafar yara kuma mafi ƙarancin shekaru a duniya," in ji Vishna Shah, Daraktar Ƙungiyar a yankin Sahel.

Ta ƙara da cewa, "Miliyoyin yara na rayuwa ne a cikin ƙaurace wa mummunan rikicin da ba za a iya misalta su ba, waɗannan yaran sun riga sun kasance za su taso a ɗaya daga cikin wuraren da ke da wahala a duniya sakamakon rasa gidajensu da al'ummominsu da duk abin da suka sani."

Ita ma ƙasar Cote d'Ivoire wacce ta fice daga yaƙin basasar da ta yi a shekarar 2011, ƙamarin da tashe-tashen hankula a yankin Sahel ke yi na shafarta, in ji ƙungiyar Save the Children.

Rikici a maƙwabciyarta Burkina Faso da Mali ya haifar da ƙaruwar yara masu neman mafaka sau goma sha biyu a ƙasar, daga kusan 2,450 a karshen shekarar 2022 zuwa kusan 29,700 a halin yanzu.

Yara su ne kashi 40 cikin 100 na mutanen da ke gudun hijira a duniya, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, amma sun fi yawa a Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Sun kai kusan kashi 58 cikin 100 na waɗanda aka tilasta musu yin gudun hijira, a cikin nazarin da Save the Children ta yi.

Ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar dai na fama da tashe-tashen hankula da juyin mulki da fatara da ƙarancin abinci na tsawon shekaru.

Mummunan cin zarafi da ake yi wa yara a cikin rikice-rikice da suka hada da kisa da raunata su da sacewa da saka yara kanana cikin ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ko kuma a matsayin sojoji ya ƙaru a cikin ƴan shekarun nan, musamman a Mali, in ji ƙungiyar Save the Children.

Haka kuma yankin Sahel na kan gaba wajen fuskantar matsalar sauyin yanayi.

AFP