Mata da 'yanmata a Gaza na rayuwa a cikin ɗaya daga cikin yanayi mafi munin bala’i jinƙai da ƙasƙanci a duniya, in ji wata babbar jami'ar Majalisar Dinkin Duniya a fannin ayyukan Mata.
Sarah Hendriks, daraktar tsare-tsare da shirye-shirye da kuma tallafin gwamnatoci a MDD, ta ce yanayin rayuwa ya zama gwagwarmaya ta yau da kullum ga mutane da yawa a yankin Falasdinu da Isra’ila ta lalata.
"Mata da 'yanmata a Gaza suna rayuwa ne a ɗaya daga cikin bala'o'i jinƙai da yanayin da ya fi tayar da hankali a duniya, inda rayuwa ta gagari mutane da dama," kamar yadda Hendriks ta shaida wa manema labarai a wani taro a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York.
Ta bayyana "goyon baya ga mata da 'yanmata a yankin Gabas ta Tsakiya" a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tashin hankali, tana mai jaddada kiran Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres na a dakatar da fadan.
Hendriks ta ce UN Women na aiki tare da ƙungiyoyin da mata ke jagoranta a Gaza don shawo kan mutanen da aka tilasta wa yin gudun hijira, da waɗanda ke fama da matsalar damuwa da kuma rashin tsaro.
"Bukatunsu sun wuce dukkan yanda ake zato. Suna buƙatar mutunci, adalci, abubuwan more rayuwa da kuma rawar da za su taka wajen sake gina makomarsu," in ji ta.
Ta jaddada cewa, dole a hada juriya da jagorancin mata a Gaza da damammaki na jinƙai, da kariya da kuma saka hannun jari na ƙasashen duniya.
















