An zaɓi Shugaban Senegal, Bassirou Diomaye Faye, a matsayin sabon shugaban Ƙungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) a ranar Lahadi.
An cimma wannan matsaya ne a yayin Taron Shugabannin Ƙasashe da Gwamnatocin ECOWAS na 69, da aka gudanar a Freetown, babban birnin Saliyo, inda shugabannin ƙasashen ƙungiyar suka zaɓe shi baki ɗaya.
ZA KU SO WAƊANNAN
Faye ya karɓi ragamar jagorancin ECOWAS daga Shugaban Saliyo, Julius Maada Bio, wanda ya riƙe wannan muƙami.
Ana sa ran Shugaba Faye zai jagoranci ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen yankin, inganta zaman lafiya da tsaro, tare da bunƙasa haɗin gwiwar tattalin arziki a faɗin Yammacin Afirka.




















