Hukumomi sun kaddamar da aikin ceto da agaji bayan wata gagarumar gobara ta ƙone kauyen da ke kan ruwa a Malaysia, inda ta lalata daruruwan gidaje.
Kusan gidaje 1,000 daga cikin kimanin 1,200 ne suka lalace a gobarar a Kampung Bahagia, wani kauye mai gidaje a kan ruwa a garin bakin teku na Sandakan a ranar Lahadi, in ji hedikwatar labarai ta gwamnati, Bernama.
Fiye da mutum 9,000 suka rasa matsuguni sakamakon gobarar.
An ƙone fili mai fadin fiye da hekta huɗu, kuma yanayin ragin ruwa a teku ya yi wahala wajen samun isasshen ruwa don aikin kashe gobara, a cewar shugaban Cibiyar Wuta da Ceton Sandakan, Jimmy Lagung.
Firaminista Anwar Ibrahim ya ce ya yi mamaki lokacin da ya ji labarin gobarar, kuma gwamnatin tarayya tare da gwamnatin jihar Sabah suna haɗin gwiwa don ba da tallafin kayayyakin buƙata da wuraren zama na wucin gadi ga wadanda abin ya shafa.
Lagung ya ce an tura ɗimbin 'yan kashe gobara zuwa wurin bayan tashar ta karɓi kiran gagagwa game da gobarar da karfe 1.32 na daren Lahadi (1732 GMT a ranar Asabar).
An ayyana wurin a matsayin yankin da bala'i ya shafa da karfe 4 na safe (2000 GMT a ranar Asabar).
An kawo ƙarshen aikin kashe gobara da ƙarfe 12 na ranar Lahadi, ba tare da rasa rai ba.
Walter Kenson, shugaban Kwamitin Kula da Bala'o'in Gundumar Sandakan, ya ce bincike da aka yi a kauyen ya gano cewa gidajen mazauna da abin ya shafa "ba su da aminci na zama a ciki."










