Burkina Faso ta faɗa a ranar Juma'a cewa ta yanke hulɗar diflomasiyya da tsohuwar ƙasar da ta yi mata mulkin mallaka, Faransa, bayan shekaru ana samun rashin jituwa, tana mai zargin Paris da ci gaba da yin ayyuka saɓanin muradun ƙasar.
"Gwamnatin Burkina Faso ta sanar wa al'ummar ƙasa da ta duniya cewa ta yanke shawarar katse hulɗar diflomasiyya da Faransa, daga yau, 26 ga Yuni, 2026," kamar yadda aka bayyana a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar ta Yammacin Afirka.
"Ba a samar da muhimman sharuɗan da za su inganta alaƙa bisa mutunta juna, da amincewa juna, da girmama ka'idar rashin tsoma baki a harkokin cikin gida, da kuma ƙarfafa matsayin ɗan ƙasa ba," in ji Ministan Sadarwa Gilbert Ouedraogo.
Ouedraogo ya ce matakin ya fara aiki a ranar 26 ga Yuni kuma ya biyo bayan sake yin nazari kan dangantaka da Paris.
Ya zargi Faransa da tallafa wa "ƙungiyoyin da ke zagon ƙasa" da "‘yanta'adda".
Ba sa mu ma'aikatar harkokin wajen Faransa ba nan-take don ta yi tsokaci kan matakin, ko da yake ta riga ta musanta zarge-zargen da ake mata na tallafa wa ta'addanci.












