| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
An sallami 'yansandan Nijeriya biyar kan zargin fashi da makami a Jihar Ribas
Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta ce ta sallami jami'an nata ne sakamakon sun shiga jerin ayyukan ta’addanci tsakanin watan Satumban 2025 zuwa Janairun 2026 a faɗin jihar Ribas.
An sallami 'yansandan Nijeriya biyar kan zargin fashi da makami a Jihar Ribas
Jami’an da aka sallama sun haɗa da John Okoi, Eyibo Asuquo, Udo Ndipmong, Bright Nwachukwu da Anele Ikechukwu. / Nigerian Police Force

Rundunar ‘yansandan Nijeriya reshen Jihar Ribas ta sallami wasu jami’anta masu muƙamin sufeto biyar da ke aiki a Sashen Ayyuka na Musamman bisa zargin hannu a fashi da makami, garkuwa da mutane, karɓar kuɗi ta tilas da haɗa baki wajen aikata laifi.

Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar a jihar, Blessing Agabe, ta fitar a ranar Jumma’a.

Kakakin rundunar ‘yansanda ta ƙasa, Anthony Placid ya ce jami’an sun shiga jerin ayyukan ta’addanci tsakanin watan Satumban 2025 zuwa Janairun 2026 a faɗin jihar Rivers.

Jami’an da aka sallama sun haɗa da John Okoi, Eyibo Asuquo, Udo Ndipmong, Bright Nwachukwu da Anele Ikechukwu.

A cewarsa, an gano lamarin ne bayan wata ƙungiya mai suna Behind Bars Human Rights Foundation ta gabatar da koke-koke a madadin mutane da dama da abin ya shafa.

Ya bayyana cewa jami’an suna amfani da ƙananan motocin haya suna gudanar da bincike ba bisa ƙa’ida ba, inda suke tare mutane da bakin bindiga.

“Jami’an suna tilasta wa waɗanda suka kama su bayyana lambobin sirrin bankinsu da bayanan asusunsu. Daga nan kuma su riƙa tura kuɗi daga asusun bankin mutanen zuwa nasu ta ƙarfin tuwo.

“Haka kuma suna ƙarya suna cewa su jami’an hedikwatar Zone 16 ne da ke Yenagoa domin tsoratar da mutane da kauce wa zargi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa bincike ya nuna cewa jami’an sun yi kuma garkuwa da wani mutum a kan titin Aba Road inda suka ƙwace Naira miliyan 3.6 da dala 4,000 daga lalitarsa ta kirifto.

Ya ce wani mutum daban kuma an yi garkuwa da shi tare da ƙwace masa fiye da Naira miliyan 7.3 da kayayyaki masu daraja, yayin da wani na uku ya rasa Naira miliyan 1.5 bayan an tare shi a kan titin NTA Road.

 

 

 

Rumbun Labarai
Nijeriya na tattaunawa da Bankin Duniya kan sabon bashin $1.25bn: rahoto
Shugaba Tinubu na Nijeriya na halartar taron Afirka da Faransa a Kenya
Rundunar Sojin Nijeriya ta musanta kashe fararen-hula a harin sama a jihar Neja
Nijeriya da Amurka sun ƙarfafa haɗin gwiwa kan tsaro da yaƙi da ta’addanci bayan ganawa a Washington
Sojin Nijeriya sun halaka ‘yanta’adda 50, sun yi asarar dakaru biyu yayin daƙile harin ISWAP a Yobe
'Yanbindiga a Nijeriya sun kashe mata masu juna biyu uku da wasu mutum 11 a Filato
Dakarun sojin Nijeriya sun kashe 'yanta'addan ISWAP da masu garkuwa da mutane
Sojojin Nijeriya sun ceto yaran da aka sace daga gidan marayu
Sanƙarau ta kashe mutum 33 a Sokoto yayin da hukumomi ke ƙoƙarin daƙile yaɗuwarta
Dangote ya sanar da shirinsa na samar da megawat 20,000  na wutar lantarki a Nijeriya
Nijeriya da Amurka sun ƙaddamar da cibiyoyin aikin tsaro don magance matsalar rashin tsaro
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda a Jihar Zamfara
Nijeriya na nuna kayan tsaro da ta ƙera a taron baje-kolin SAHA 2026 da ke gudana a Istanbul
Kwamitin wucin-gadi na Majalisar Dokokin Nijeriya zai je Afirka ta Kudu kan batun ƙyamar baƙi
Jam'iyyar NDC ta miƙa takarar shugaban ƙasa ga kudancin Nijeriya, in ji Buba Galadima
Nijeriya za ta fara kwaso 'yan ƙasar daga Afirka ta Kudu saboda rikicin ƙyamar baƙi
Peter Obi ya bayyana shirin ficewa daga jam'iyyar ADC
Ba mu yanke shawara kan makomarmu ta siyasa ba – Kwankwaso
Sojojin Nijeriya sun lalata maɓoyar 'yan Boko Haram a Sambisa, sun kashe 'yan ta'adda masu yawa
An kama 'yan Nijeriya 62 a Uganda kan zargin gudanar da coci ba bisa ƙa'ida ba