Burkina Faso da Mali da kuma Nijar sun soma wani shiri da zai ɗauki shekara ɗaya na ficewa daga Kotun hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC), a cewar sanarwar Kotun.
A watan Satumban 2025 ne ƙasashen Afirka ta Yamma uku suka sanar cewa za su fice daga kotun ICC, bayan sun yi zargin cewa manyan ƙasashe suna amfani da ita wajen "danniya da mulkin mallaka na zamani."
ICC ita ce kotun da ke yaƙi da manyan laifuka a duniya, wadda ke da alhakin gurfanar da mutanen da ake zargi da kisan ƙare-dangi, da cin zarafin bil'adama, da yaƙi da kuma laifukan take hakkin bila’ada da dokokin kotunan ƙasa ba za su iya ɗaukar mataki ba.
A cikin sanarwa da kotun ta fitar ranar Laraba, shugaban hukumar gudanarwa ta ICC ya tabbatar da cewa Mali, Burkina Faso, da Nijar sun gabatar da wasiƙun janyewa daga cikinta kuma sun fara aiwatar da tsarin ficewa na tsawon shekara ɗaya kamar yadda yarjejeniyar da ta kafa ICC ta tanada.











